-
Handala Ta Mika Bayanan Jami'ai Da Sansanonin Sirri Na Amurka Ga Irgc
Handala a cikin wata sanarwa ta bayyana cewa bayanan da suka shafi jami'an da ke cikin rundunar sojan ruwa na Amurka da kuma wuraren da sansanonin sirrinsu suke a yankin, suna hannun wannan kungiya sirrin.
-
Bin Fikirar Imam Khumaini Ne Hanyar Samun Mafita Ga Al'umma - Jagora Sheikh Zakzaky (H) + Hotuna
A yayin tunawa da wafatin Imam Khumaini (QS), Sheikh Zakzaky (H) ya gabatar da jawabi a taron Makon Imam Khumaini da Dandalin Ɗalibai na Harkar Musulunci suka shirya karo na 37, da yammacin ranar Talata 16 ga Zhul Hijja 1447, a gidansa da ke Abuja.
-
Iran Ta Kai Hari Kan Jirgin Ruwa, Hedkwatar Rundunar Sojan Ruwa Da Sansanin Jiragen Sama Na Amurka
Rundunar Tsaro ta Juyin Musulunci (IRGC) ta sanar da cewa dakarunta sun kai hare-haren ramuwa kan wani jirgin ruwan Amurka, hedkwatar Rundunar Sojan Ruwa ta Amurka ta Biyar a Bahrain, da kuma wani sansanin jiragen sama na Amurka a yankin, biyo bayan ayyukan ta'addanci guda biyu na Amurka da suka kai wa kadarorin Iran.
-
Ƙungiyar Larabawa Ta Yi Allah Wadai Da Kutse Da Sahyuniyya Suka Yi Wa Masallacin Aqsa
Ƙungiyar Larabawa ta yi kakkausar suka ga kutsawar da maziyartan Sahyuniyya masu tsattsauran ra'ayi suka yi wa Masallacin Al-Aqsa, wanda aka sanya karkashin kariyar sojojin mamaya na Isra'ila.
-
Jiragen Marasa Matuki Na Hizbullah Sun Ci Gaba Da Zama Babbar Barazana Ga Sojojin Isra'ila
A cewar kafafen yada labarai na Isra'ila, ayyukan nasara na jiragen marasa matuki na Hizbullah sun janyo damuwa ga sojojin Isra'ila, kuma an fara bincike kan waɗannan hare-haren.
-
Taliban: Tattaunawar A Fakaice Da Pakistan Na Ci Gaba, Bukatun Islamabad Ba Ma Su Yiwuwa Ba Ne
Gwamnatin riƙon kwarya ta Afghanistan ta ce bayan dakatar da tattaunawar kai tsaye da Pakistan, tuntuɓar a fakaice tana ci gaba, amma saboda "bukatu marasa ma'ana" na Islamabad ba a samu ci gaba ba. Kabul ta jaddada cewa bukatarta ita ce mutunta ikon Afghanistan da kuma dakatar da hare-haren kan iyaka, kuma a lokaci guda tana musanta zargin Pakistan game da kasancewar TTP a cikin ƙasar Afghanistan.
-
Hare-Hare 36 Na Isra'ila Sun Shahadantar Da Mutum 12 Tare Da Raunata 35 A Kudancin Lebanon
A cikin hare-haren da gwamnatin Sahyuniyya ta kai a daren Lahadi da safiyar Litinin a garuruwa da kauyukan kudancin Lebanon, wanda ya faru fiye da sau 36, mutum 12 sun shahada sannan 35 dukansu sun jikkata.
-
Rahoto Cikin Hotuna | An Gudanar Da Taron Kusantar Addini Da Al'adu A Zauren Majalisar Ahlul Bayt (A.S) A Qum
Rahoto Cikin Hotuna | An Gudanar Da Taron Kusantar Addini Da Al'adu A Zauren Majalisar Ahlul Bayt (A.S) A Qum
-
An Fassara Tare Da Buga Littafin "Imam Ali (A.S) A Mahangar Halifofi" Da Harshen Swahili
Bisa daukar nauyin Babban Daraktan Ayyukan Al'adu da Bugawa na Majalisar Ahlul Bayt (A.S), an fassara tare da buga littafin "Imam Ali (A.S) a mahangar Halifofi" da harshen Swahili.
-
Ilhan Omar: Isra'ila Ta Bayar Da Umarnin Gudanar Da Tsarin Da Tai A Gaza Akan Labanon
‘Yar majalisar dokokin Amurka 'yar Democrat kuma musulma a cikin wani sako ta bayyana cewa Tel Aviv tana aiwatar da tsarin Gaza a Labanon, ba tare da wani kariya ba, kuma ta jaddada taken cewa: "Babu wani taimakon Amurka ga Isra'ila".
-
Rahoto Cikin Hotuna | Atabal Alawiyya Ta Gudanar Da Bikin Ɗaga Babbar Tutar Ghadir A Iraqi
Manzon Allah (Sawa): Wanda Na Kasance Shugabansa Ne, To Wannan Alin Ma Shugabansa Ne
-
IRGC Sun Kai Hari Kan Jirgin Ruwan Amurka Da Makami Mai Linzami Na Cruise
Sojojin Ruwa Iran sun mayar da maratani ga harin da Amurka ta kai ga wani jirgin kasar in da suka kai hari kan jirgin ruwa mai suna "MSC Sariska" mai alaka da Amurka da Isra'ila da makami mai linzami na Cruise.
-
Isra’ila Ta Janye Kai Harin Bama-Bamai Kan Labnon Bayan Iran Ta Yi Gargadi
Kafofin yada labaran Isra'ila sun sanar da cewa sojojin wannan gwamnati sun kasance a gab da kai wani gagarumin hari a yankin Dahieh ta kudancin Beirut da kuma cibiyoyin kwamandancin Hizbullah, amma a cikin mintuna na ƙarshe kuma biyo bayan matsin lamba da shiga tsakani na Amurka, an dakatar da aikin.
-
Ar-Riyadh: Hadarin Yaƙin Lebanon Yana Barazana Ga Dukan Yankin Da Duniya Baki Ɗaya Ne
Wata jaridar Saudiyya ta rubuta cewa abubuwan da ke faruwa a Lebanon sun haifar da shakku mai tsanani game da tsarin kasa da kasa, kuma hadarinsa ya wuce fagen cikin gida da yanki, yana barazana ga tsarin kasa da kasa.
-
IRGC Sun Mai Martanin Kan Sansanin Sojin Da Amurka Ta Kawo Kan Tsibirin Iran
Dakarun Juyin Musulunci na Iran sun kai hari kan sansanin sojan sama wanda daga shi ne Amurka ta kai hari a kan hasumiyar sadarwa a tsibirin Sirik da ke lardin Hormozgan.
-
Rundunar Sojin Iran ta Bayyana Wani Sabon Jirgin Ruwan Yaƙi Mai Ci Gaba
An buɗe jirgin ruwan hari mai sauri mai suna "27 Rajab", wani jirgin ruwa ne da ya dogara da ƙirar "Trimaran" kuma yana da ƙarfin yaƙi na ci gaba wanda ke nuna wani sabon mataki na haɓaka ƙarfin sojan ruwa na Iran.
-
Raj'a (Dowawa Duniya) A Aƙidar Shi'a A Cikin Littattafan Addinai Na Sama
Raj'a tana a ma'ana dawowar gungun waɗanda suka mutu zuwa duniyar nan kafin a tayar da kiyama, da nufin taimakawa wajen kafa gwamnati ga muminai, ko kuma ga azzalumai da kafirai domin su ga kafuwar gwamnatin ƙarshe ta gaskiya, yana daga cikin aƙidun Shi'a. Wannan imani wanda ya samo asali daga dalilai daban-daban na Alƙur'ani da hadisai, an kuma bayyana shi a cikin sauran littattafan sama kamar Attaura da Linjila, lamarin da ke nuna dayantar tawhidi na waɗannan aƙidu.
-
Labarai Cikin Bidiyo | Yadda Hizbullah Ta Kai Hari Kan Wata Motar Sojojin Isra'ila Hari A Al-Jalil
Kamfanin Dillancin Labarai na Ahlul-Bayt (a.s) na Duniya – ABNA – A rahoton ta Hizbullah ta fitar da hotunan bidiyo na lokacin da jirginta maras matuki na kunar bakin wake ya kai wa motar sojojin gwamnatin yahudawa hari a yankin Al-Jalil da ke arewacin Falasdinu da Isra’ila ta mamaye.
-
Da'awar Isra'ila Na Sarrafa Ginin Ganuwar Al-Shuqif Farfaganda Ce Kawai Ba Nasarar Soji Ba
Sojojin Isra'ila da safiyar yau Litinin sun yi da'awar cewa sun kwace iko Ganuwar Al-Shuqif (Beaufort) a kudancin Lebanon. Amma manazarta da masu fafutukar kafofin watsa labarai sun ɗauki wannan matakin a matsayin farfaganda da ƙoƙarin Isra'ila don nuna nasara a kan abubuwan da suka faru a baya, sun jaddada cewa gwagwamayar Lebanon na ci gaba da addabar makiya tare da sabbin dabarun yaki da suka hada da ɓoyewa da hare-hare cikin sauri da jirage mara matuki da makamai masu linzami.
-
Hizbullah Na Ƙara Tsaurara Hare-Harenta A Kudancin Lebanon
Isra’ila Na Shan Azaba A Hare-Haren Jirage Marasa Matuki Na Hizbullah
Hare-haren jirage marasa matuka na baya-bayan nan da Hizbullah ta kai a layin iyakar Kudancin Lebanon, wanda ya jawo asara ga sojojin Isra'ila, ya mayar da yanayin rikicin yankin zuwa wani sabon mataki. Yadda Hizbullah ta fara amfani da rundunarta ta jiragen mara matuki wajen ƙara matsin kai farmaki a filin daga, ya sa Isra'ila ta sake duba manufofinta na tsaron sama na yau da kullun
-
Hizbullah Ta Kai Harin Rokoki Kan Rukunin Soji Na Isra'ila A Haifa
Hizbullah ta bayyana cewa mayakan gwagwarmayar Musulunci sun kai hari da rokoki kan rukunin sojin Isra’ila a Haifa.
-
Labarai Cikin Bidiyo | Yadda Hizbullah Ta Kai Hari Kan Motar Hamer Kwamandoji
Kamfanin Dillancin Labaran ƙasa da ƙasa na Ahlul-Baiti (AS) – ABNA - ya habarta cewa: kafar yada labaran yaki na gwagwarmayar Musulunci sun fitar da bidiyon yadda suka kai hari kan wata motar Hamer ta kwamandoji da ke dauke da sojojin Isra'ila a sansanin Al-Manara da ke kan iyakar kudancin Lebanon, ta hanyar amfani da jirgin Ababil.
-
Sayyid Zakzaky (H) Ga ‘Yan Uwa Ya Kamata A Kowace Ɗabi'a A Gan Mu Da Kyakkyawa
Wannan bayanin tsakure ne daga Littafin “TASIRIN ƊABI’U” na Shaikh Ibraheem Zakzaky (H) Wallafar cibiyar wallafa da yaɗa ayyukan Shaikh Zakzaky (H).
-
Afganistan: Mutane 18 Sun Mutu, 29 Sun Jikkata A Hatsarin Mota A Laghman
Sakamakon kifewar wata babbar mota da ke dauke da 'yan ci-rani da suka dawo daga Pakistan a lardin Laghman na Afghanistan, mutane 47 ne abun ya shafa jumullar wadanda suka mutu da jikkata.
-
Hizbullah Ta Kai Hari Makami Mai Linzami Zuwa Kiryat Shmona Da Na’urar Tsaro
Sanarwar safiyar yau ta Hizbullah: A cikin sa'o'i 24 da suka gabata, mayakan gwagwarmayar Musulunci, a matsayin martani ga keta yarjejeniyar tsagaita wuta daga Isra'ila da hare-hare kan fararen hula, da ruguza gidaje da kauyuka a kudancin Lebanon, sun aiwatar da ayyukan soji guda 22 a kan matsugunai da kayan aikin sojojin Isra'ila.
-
Hizbullah Ta Fara Farautar Kwamandoji Da Jiragen Matasan Marasa Matuki
Gidan Rediyon Sojojin Sahayoniyya: A daren jiya an harba rokoki 15 daga Lebanon zuwa garuruwan arewacin Isra'ila, daya daga cikinsu ya kai hari kai tsaye a wata cibiyar kasuwanci.
-
Iran: Karya Yarjejeniyar Tsagaita Wuta Da Cin Zarafin Fade Da Isra'ila Ke Yi Laifukan Yaki Ne
Mataimakin Ministan Harkokin Waje na Iran a Harkokin Shari'a da Ƙasashen Duniya, Kazem Gharibabadi, ya soki Isra'ila sosai game da martanin da ta bayar kan sanya sunanta a cikin jerin Majalisar Ɗinkin Duniya game da Fade, yana mai cewa gwamnatin Tel Aviv tana gujewa hukunci ta hanyar kai hari ga cibiyoyin duniya.
-
Iran Ta Kakkabo Jirgi Maras Matuki Na Amurka A Kewayen Tsibirin Qeshm
Rundunar tsaron sararin samaniya ta sojojin Iran ta kakkabo wani jirgi maras matuki na abokan gaba a kewayen Qeshm.
-
Adadin Wadanda Suka Shahada A Hare-Haren Da Isra'ila Ta Kai A Lebanon Ya Kai 3,324
Adadin wadanda su kai shahada a hare-haren da sojojin mamaya na Isra'ila suka kai wa Lebanon tun daga ranar 2 ga Maris, duk da yarjejeniyar tsagaita wuta, ya karu da 55, inda ya kai 3,324.
-
Hizbullah Ya Aiwatar Da Ayyuka 19 A Kan Sojojin Mamayar Isra'ila A Kudancin Lebanon
Hizbullah ta fitar da wata sanarwa inda ta bayyana aiwatar da ayyukan hare-hare 19 kan tarukan sojoji, motocin yaƙi, da daidaikun sojojin Isra'ila a kudancin Lebanon. Domin kare Lebanon da al'ummarta, tare da mayar da martani ga keta yarjejeniyar tsagaita wuta da Isra’ila ke yi, hare-hare kan fararen hula da lalata gidajensu da ƙauyukansu.