5 Janairu 2026 - 21:41
Source: ABNA24
Isra'ila Ta Kai Munanan Hare-Hare A Kudancin Lebanon

Gwamnatin Isra'ila ta kai manyan munanan hare-haren da a yankuna daban-daban a kudancin Lebanon

Kamfanin Dillancin Labaran ƙasa da ƙasa na Ahlul-Baiti (ABNA) ya habarta cewa: Sojojin Isra'ila sun sanar da cewa sun kai hari kan wasu wurare da suka yi ikirarin mallakar Hamas da Hizbullah ne a yankuna daban-daban na Lebanon.

Majiyoyin labarai sun ruwaito a yau Litinin cewa gwamnatin Isra'ila ta kai hari kan kauyen Ain Al-Tina a yankin Bekaa a gabashin Lebanon.

Kafofin watsa labaran Isra'ila sun kuma sanar da cewa sojojin sun kai hari kan kudancin Lebanon.

Kamar yadda Wakilin Al-Jazeera ya bayyana cewa gwamnatin Isra'ila ta kuma kai hari kan kauyen Anan a birnin Jizin a kudancin Lebanon.

Ya ce Isra'ila ta kai hari kan kauyukan Ain Al-Tina da Al-Manara a yankin Bekaa a gabashin Lebanon da kuma Anan a kudancin Lebanon a manyan hare-hare uku.

Sojojin Isra'ila sun yi ikirarin cewa sun kai hari kan wasu wurare na Hamas da Hizbullah a Lebanon.

Isra'ila ta kai hari kan kauyen Kafrahti a kudancin Lebanon.

Bayanan nan, rundunar sojin Isra'ila ta sanar da cewa tana da niyyar kai hari kan wasu wurare da ta yi ikirarin mallakar Hizbullah ne.

Your Comment

You are replying to: .
captcha