-
Manazarcin Tsaro Kuma Masanin Harkokin Bayanai:
hidimaNazari: CIA Tana Aiki Ne Ga Isra'ila, Ba Don Amurka Ba
John Kiriakou, manazarcin tsaro kuma masanin harkokin bayanan sirri, yana mai suka mai tsanani game da yanayin da CIA ke ciki a yanzu, ya yi iƙirarin cewa wannan hukuma ta shiga cikin tasirin…
Sabbin labarai
-
Manazarcin Tsaro Kuma Masanin Harkokin Bayanai:
hidimaNazari: CIA Tana Aiki Ne Ga Isra'ila, Ba Don Amurka Ba
John Kiriakou, manazarcin tsaro kuma masanin harkokin bayanan sirri, yana mai suka mai tsanani game da yanayin da CIA ke ciki a yanzu, ya yi iƙirarin cewa wannan hukuma ta shiga cikin tasirin ƙungiyoyin yahudawa sosai, kuma maimakon ta ci gaba da anfanar manufofin ƙasar Amurka, tana aiki ne don cimma manufofin Isra'ila.
-
hidimaUNOCHA: Karancin Kasafin Kuɗi Yana Barazana Ga Ayyukan Ciwarwa Ga Yara Da Mata Miliyan 5.7 A Afganistan
Ofishin Gudanar da Taimakon Bil'adama na Majalisar Ɗinkin Duniya ya yi gargadin cewa, karancin albarkatun kuɗi ya sanya samun damar yara da mata miliyan 5.7 a Afganistan ga ayyukan lafiya da abinci na yau da kullun cikin hadari mai tsanani.
-
hidimaMDD: Ta Jaddada Buƙatar Ɗaukar Matakin Gaggawa Don Tallafawa Mata Da 'Yan Mata Na Afganistan
Shugaban ofishin sashen mata na Majalisar Ɗinkin Duniya, a ziyararsa zuwa Afganistan, ya tattauna da jami'an Taliban da abokan huldar diflomasiyya game da ƙara tallafawa mata da 'yan mata, da kuma cire ƙuntatawa da aka sanya wa ma'aikatan mata na hukumomin jin kai.
-
Tonon Silili Yadda 'Yan Ƙasar Italiya Kusan 1,000 Su Kai Tarayya A Kisan Kiyashin Gaza
hidimaHannun Kasar Italiya Dumu-Dumu A Kisan Kiyashin Da Isra’ila Ke Yiwa Falasdinawa
Bayanan hukumar ma'aikatar yaƙi na gwamnatin yahudawa da aka buga kwanan nan, sun nuna cewa 'yan ƙasar Italiya 928 sun shiga cikin kisan kiyashin da Isra’ila k yi a zirin Gaza daga Oktoba 2023 zuwa Maris 2025. Bayyana waɗannan takardun, waɗanda ke nuna haɗin gwiwar Rome da Tel Aviv fiye da dangantakar hukuma, ya haifar da cece-kuce mai yawa a cikin muhawarru na siyasa na Italiya, kuma Stefania Ascari, 'yar majalisar Italiya, ta zargi gwamnatin ƙasarta da gujewa daukar alhakin hakan.
-
batu na musammanAl Khalifa Da Yaƙi Da Al'amuran Addini; 'Yan Shi'a Ba Sa Mika Wuya A Tarihi
Bahrain, a gab da lokutan tarukan addini, ta sake fuskantar ƙuntatawa na gwamnati a kan al'amuran addini na 'yan Shi'a; ƙuntatawa waɗanda, a ganin masu lura, sun wuce iyakar da aka "tsara" kuma sun zama fagen sarrafawa da takaita ayyukan addini. Duk da haka, shaidun tarihi da zamantakewa sun nuna cewa al'ummar Shi'a ta Bahrain na ci gaba da tabbatuwa da kiyaye asalin addini da al'amuran Imam Husaini As.
-
batu na musammanBahrain: Hanawar Hukuma Ga Halartar Arba’een Bai Hana Su Nuna Bakin Cikinsu Ba Ga Shahadar Imam Husain As
Yayin da Arba'in na Hussaini ke gabatowa, hana 'yan Shi'a na Bahrain tafiya zuwa wuraren ibada masu tsarki, ya haifar da kwararar bayyana ƙaunar da baƙin ciki a tsakaninsu; dubban 'yan Bahrain waɗanda kowace shekara sukan isa Karbala, a wannan shekara, saboda haramcin tafiyar a hukumance, sun yi tafiya zuwa Arba'in da zukatansu kawai.
-
hidimaYahudawa Na Kai Harin Dabbancin Kan Fursunonin Matan Falasdinu A Kurkukun Al-Damun
Cibiyoyin kula da al'amuran fursunonin Falasdinu a yau (Lahadi) sun ba da rahoton faruwar wani aikin danniya mai tsanani a kan fursunonin mata na Falasdinu a kurkukun Al-Damun. Dangane da wannan rahoto, sojojin gwamnatin mamaya, ta hanyar kutsawa sashen mata a tsakiyar daren Juma'a, ta amfani da hayaki mai sa hawaye, duka da wulakanci, sun haifar da shaƙewar numfashi da kuma tsananta yanayin raunin jiki na wasu daga cikinsu. A halin yanzu, mata 94 na Falasdinu, ciki har da mata biyu masu juna biyu da marasa lafiya biyu masu ciwon daji, suna cikin wannan kurkuku.
-
hidimaAyyukan Ta’addancin Yahudawa Na Kara Tsamari Bayan Kona Masallatai A Nablus Da Tulkarm
Ma'aikatar Harkokin Waje ta Hukumar Falasdinu, yayin da take yin Allah wadai da aikin yahudawa na kona masallatai biyu a ƙauyukan "Qasra" (Nablus) da "Kur" (Tulkarm), ta jaddada cewa waɗannan hare-hare suna faruwa ne tare da goyon bayan gwamnatin mamaya na Isra'ila kai tsaye, kuma saboda kariyar da ake bas u na rashin hukunta sun daga hukumar ne yasa suke wuce gon a da iri, kuma ta buƙaci al'ummar duniya ta ɗauki matakai masu tasiri da tilaswa don dakatar da waɗannan ta'addanci.
-
hidimaRahoto Cikin Hotuna | Na Taron Tunawa Da Shahida Zahra Haddad Adel A Tehran
Rahoto Cikin Hotuna | Na Taron Tunawa Da Shahida Zahra Haddad Adel A Tehran
-
Menene Amurka Ta Yi Hasara a Makon Da Ya Gabata?
hidimaGirman Asarar Amurka A Fafatawar Mako Guda Da Iran
Rahotannin da kafofin watsa labarai na kasashen yamma suka buga a 'yan kwanakin nan sun nuna cewa fafatawar baya-bayan nan da Iran, ta haifar da hasarar rayuka da soji mai yawa ga Amurka a yankin, kuma ta yi tasiri ga lissafin rashin dabarar yakin Washington.