-
hidimaFuskantar Jahiliyya Ta Zamani, Nauyi Ne Na Da Ya Hau Kan Duniyar Musulunci
Dokta Pezeshkian, yana mai nuni da gargadin jagoran shahidi game da sake haifar da jahiliyya a duniya ta zamani, ya kara da cewa: "Imam Shahidi Ayatullah Khamene'i ya shafe shekaru yana gargadin…
Sabbin labarai
-
hidimaFuskantar Jahiliyya Ta Zamani, Nauyi Ne Na Da Ya Hau Kan Duniyar Musulunci
Dokta Pezeshkian, yana mai nuni da gargadin jagoran shahidi game da sake haifar da jahiliyya a duniya ta zamani, ya kara da cewa: "Imam Shahidi Ayatullah Khamene'i ya shafe shekaru yana gargadin cewa jahiliyya ba ta takaita da zamanin kafin Annabi kawai ba. Kimiyya na iya ci gaba, fasaha na iya sarkaka, kuma kayan aikin iko na iya girma, amma idan mutuncin dan Adam ya bace, wani sabon salo na jahiliyya zai taso. A cikin jawaban da suka shafi mab'as, fuskantar Annabi da jahiliyya da yuwuwar sake haifar da ita a duniya ta zamani, na daga cikin abubuwan da jagoran shahidi ya sha yin magana akai."
-
hidimaBabu Wata Kasa Ta Musulunci Da Ta Kamata Ta Zama Dandalin Kai Hari Ga Wata Kasa Ta Musulunci
Shugaban ƙasa, yana nuni da wani bangare na wasiyyar Amiral-Mu'minin, ya kara da cewa: "Imam Ali (AS) ya ce, 'Ina wasiyyar ku da dukan 'ya'yana da iyalina da duk wanda wasikata ta kai gare shi, da taqawa, da tsara al'amarinku, da gyara dangantakarku, domin na ji kakanku (SAW) yana cewa: Gyara dangantaka ya fi sallar nafila da azumin nafila'. Gyara dangantaka da samar da hadin kai a tsakaninmu ya fi sallah da azumi. Idan Iran ta kare Falasdinu, ta kashe kudi, ta tsaya tsayin daka a kan mamaya, ba ta daukar wadannan ayyuka a matsayin wani gata don neman wani gata daga wasu ba, a'a, tana daukar su a matsayin wani hakki na Musulunci. Musulunci da muka sani ba ya ba da izini idan wanda aka zalunta ya nemi taimako, mu fara tambayar mazhabarsa, addininsa, da imaninsa."
-
Dokta Pezeshkian A Taron Kasa Da Kasa Na 40 Na Hadin Kan Musulunci:
hidimaIran: Hadin Kai Ba Shiri Ba Ne, Dabaru Ce Ga Al'ummar Musulunci
Shugaban ƙasar Iran, yayin da ya jaddada cewa hadin kan Musulunci ba yana nufin zama nau’I daya na Musulmai ba, ya bayyana cewa mayar da damarmakin da ke warwatse a duniyar Musulunci zuwa ga niyya da iko na gama-gari, ya dogara ne kan sarrafa sabani, bin adalci, tabbatar da tsaro na juna, da fadada hadin gwiwar kimiyya da tattalin arziki tsakanin kasashen Musulunci.
-
hidimaMahangar Imam Ali (AS) Game Da Yaki Da Zaman Lafiya / Zaman Lafiya Bisa Hikima Ko Kaskanci?
Yaki da zaman lafiya bisa hikima, tushen karbabben Musulunci ne kuma ya dogara da tsarin mulkin Amiral-Mu'minin (AS) a mu’amalarsa da kasashe daban-daban; don haka yaki marar amfani yana jawo gajiyawar sojoji, kuma zaman lafiya marar hikima yana ba da damar mika wuya ga mulkin mallaka.
-
hidimaJami’an Diflomasiyya Na Ƙoƙarin Farfado da Tattaunawar Tehran da Washington
A daidai lokacin da ake ci gaba da ƙoƙarin diflomasiyya don sake bude hanyar tattaunawa tsakanin Iran da Amurka, hankula sun karkata ga mashigin Hormuz; wata hanya mai dabaru inda 'yancin zirga-zirgar jiragen ruwa a cikinta da kuma yadda za a rage tashin hankali suka zama muhimman abubuwan da ake tattaunawa a shawarwarin da ke gaba.
-
A Jajiberin Shekara Ta 1501 Da Haihuwar Annabin Musulunci (Saw);
al'aduAn Buga Babban Littafi Mai Suna "Bisharar Littafi Mai Tsarki Game Da Zuwan Annabi Mai Girma Da Imaman Tsarkaka" + Hoto
Wannan littafi, wanda ya mayar da hankali kan batun bishara da alamun zuwan Annabin Musulunci (SAW) a cikin litattafa masu tsarki na baya, yana bayyana muhimmancin tattaunawa tsakanin addinai da kuma nazarin matsayin Annabin Rahma a cikin addinan Allah.
-
A Karon Farko;
hidimaJamus Zata Samawara Da Sojoji Musulmi 3,000 Malaman Addinin Musulunci
Ma'aikatar Tsaro ta Jamus ta sanar da cewa zuwa karshen shekara ta 2026, a karon farko za ta dauki limaman Musulunci don ba da hidimomin addini ga sojojin Musulmi na kasar; matakin da ya zo bayan shekaru da yawa na samun irin wannan hidima ga sojojin Furotesta, Katolika da Yahudawa.
-
hidimaIran: Araghchi Ya Karbi Bakuncin Ministan Harkokin Wajen Qatar
Ministan harkokin wajen Qatar ya ziyarci Tehran da yammacin yau, inda ya gana da takwaransa na Iran kuma ya tattauna da shi.
-
hidimaLabarai Cikin Hotuna | Na Bude Taron Hadin Kan Musulunci Na Kasa da Kasa Karo Na 40
An fara taron kasa da kasa na 40 na hadin kan Musulunci da safiyar yau, tare da halartar shugaban ƙasa da wasu malaman duniyar Musulunci a zauren taron shugabannin a Tehran.
-
al'aduYadda Zagayen Mauludi Ya Gudana A Katsina + Hotuna
Da misalin ƙarfe 9:00 na safiyar Talatar 12 ga watan Rabi’ul Awwal, 1448H, wanda ya yi daidai da 25 ga watan Agusta, 2026, ’yan’uwa Musulmi almajiran Sayyid Ibrahim Zakzaky (H) na garin Katsina suka fito ƙwai da kwarkwata don nuna murnarsu da zagayowar ranar haihuwar Manzon Rahma (S).