3 Janairu 2026 - 11:22
Source: ABNA24
IRGC: Trump ya yi Barazana Ne Ga Al'umma Da Jamhuriyar Musulunci Saboda Yanke Kauna

Rundunar Tsaron Juyin Juya Halin Musulunci ta jaddada a cikin wata sanarwa a munasabar taron cika shekaru da shahadar Janar Suleimani: Rushewar ikon siyasa da tsaro na tsarin mulkin mallaka da rugujewar tsarin Amurka a yankin da duniya baki ɗaya ya samu ne sakamakon tasirin wannan shahidi da mayakan gwagwarmaya. 

Rundunar Tsaron Juyin Juya Halin Musulunci ta jaddada a cikin wata sanarwa a munasabar taron cika shekaru da shahadar Janar Suleimani: Rushewar ikon siyasa da tsaro na tsarin mulkin mallaka da rugujewar tsarin Amurka a yankin da duniya baki ɗaya ya samu ne sakamakon tasirin wannan shahidi da mayakan gwagwarmaya.

Trump da Netanyahu mai sha jini, ta hanyar kashe wannan shahidi cikin tsoro, ba su iya lalata ikon Allah dake kunshe ga wannan shahidi da hanyarsa da aikinsa ba, domin, duk da kisan gillar da suka yi masa cikin tsoro. da mayakan Falasdinawa ba su ƙirƙiri "Guguwar Al-Aqsa" ba, wacce take hanya ce da suka koya daga shahidi Suleimani.

A duk da haka kuma, al'ummar Iran, ta hanyar yin taka tsantsan da rashin shiga cikin masu tayar da zaune tsaye, sun dakile shirin miyagun shugabannin Amurka da 'yan amshin shatansu masu cin amana, kuma sun yi musu mummunan mari a fuska, wanda yanzu fushin Trump ya mamaye shi ya zamo yana barazana ga al'umma da gwamnatin Jamhuriyar Musulunci saboda rashin fatan samun nasara akansu.

Your Comment

You are replying to: .
captcha