-
Shugaban Hukumar Leken Asirin Turkiyya Ya Gana da Wakilan Hamas Kan Yarjejeniyar Tsagaita Wuta A Gaza
Shugaban Hukumar Leken Asirin Turkiyya ya gana da Khalil al-Hayya, shugaban tawagar tattaunawa ta Hamas, da tawagarsa da ke rakiya a Istanbul domin tattauna ci gaban yarjejeniyar tsagaita wuta ta Gaza.
-
Hashdush Sha’aby: ta yi kira da a fito tattaki don tunawa da ranar shahadar Shahid Qasim Da Muhandis
Kungiyar ta yi wa al'ummar Iraki jawabi kai tsaye, tana mai tabbatar da cewa fitowar dimbin jama'a fili suna nuna matsayinsu ba tare da wata rufa-rufa ba, da sabunta alkawarin da ba ja baya sakone mai karfi cewa tafarkin shahidai yana ci gaba mai wanzuwa ne, kuma jinin da ya kare Iraki ba zai taba yin kasa a gwiwa ba. Sun jaddada cewa duk wanda ya yi imanin cewa kisan kai zai kawo karshen wannan yunkuri ya yi kuskure kwarai da gaske.
-
Hizbullah Ta Iraki Ta Mayar Da Martani Ga Qudirin Kwace Makamai Gwagwarmaya
Hizbullah ta Iraki ta sake nanata kin amincewarta da duk wani magana na kwace makamai daga hannun 'yan gwagwarmaya.
-
An Rusa Kungiyar 'Yan Ta'adda Ta ISIS A Kudancin Damascus, An Kama Shida, Har Da Shugabanta
Ma'aikatar Harkokin Cikin Gida ta Siriya ta sanar da wargaza wata kungiyar 'yan ta'adda ta ISIS a yankin Daraya da ke kudancin Damascus tare da kama wasu 'yan ta'adda shida, ciki har da shugabanta.
-
Sun Toshe Manyan Hanyoyin Mota Da Taraktoci
Manoman Girka Suna Ci Gaba Da Zanga-Zangar Neman Biyan Hakkokinsu
Manoman Girka sun ci gaba da zanga-zangar adawa da gwamnati a ranar Lahadi, sun taru da taraktocinsu a wurare masu mahimmanci a manyan hanyoyin kasar.
-
Kisan Da Aka Yiwa Yahudawa Shiri Ne Na Isra’ila Don Nuna Ana Kyamar Yahudawa
Janar Mousawi: Kisan Yahudawa Wani Aiki Ne Na Yaudara Da Gwamnatin Sahyuniya Ta Yi Don Nuna Ana Kyamar Yahudawa
-
Koriya Ta Arewa Ga Japan: Da'awar Tallafawa Zaman Lafiyar Duniya Ba Ta Da Alaƙa Da Kokarin Samar Da Nukiliya
Darektan Cibiyar Nazarin Japan a Ma'aikatar Harkokin Waje ta Jamhuriyar Demokradiyyar Koriya ya bayyana cewa sabuwar gwamnatin Japan tana bin manufofin soja mafi haɗari da tsauri idan aka kwatanta da gwamnatocin da suka gabata.
-
Al’ummar Morocco Sun Yi Zanga-Zangar Kin Amincewa Da Daidaitawa Da Isra'ila.
Al’ummar Morocco Sun Yi Zanga-Zangar Nuna Goyon Falasdinu
Dubban 'yan Morocco sun yi zanga-zangar a daren Asabar don nuna goyon baya ga mutanen Gaza da ake zalunta, da kuma kin amincewa da daidaita dangantaka da gwamnatin Isra’ila.
-
Netanyahu Na Shirin Yi Wa Trump Bayani Kan Shirin Yiwuwar Sabbin Hare-Hare Kan Iran
Kafafen Yada Labarai Na Amurka Sun Yi Ikirarin Game Da Sabuwar Ganawar Da Netanyahu Da Trump Suke Kokarin Yi | Sabon Mummunan Mafarkin Tel Aviv Game Da Makamai Masu Linzami Na Iran
-
Labarai Cikin Hotuna | Ziyarar Sheikh Zakzaky H Kabarin Shahidai A Behesht-E-Zahra (A.S.)
Kamfanin Dillancin Labaran ƙasa da ƙasa na Ahlul-Baiti (ABNA) ya habarta cewa: Sheikh Ibrahim Zakzaky H, Babban Shugaban Harkar Musulunci ta Najeriya, ya ziyarci kaburburan shahidai, ciki har da Janar Baqeri, a lokacin ziyararsa zuwa Iran.
-
Kamfanonin A Birtaniya Suna Ɗaukar Sojojin Haya Na Colombia Don Yaƙi A Sudan
Binciken da Guardian ta yi ya nuna cewa kamfanonin da suka yi rijista a Burtaniya sun ɗauki ɗaruruwan sojojin haya na Colombia don yaƙi tare da Rundunar Gaggawa a Sudan.
-
Labarai Cikin Hotuna | Taron Manema Labarai Cika Shekaru Shida Na Tunawa Da Shahid Hajj Qasem Suleimani
An gudanar da taron manema labarai na cika shekaru shida na tunawa da shahidi Hajj Qasem Suleimani a safiyar yau, Asabar (20 ga Disamba, 2025), tare da halartar Abbas Ali Kadkhodaei, kakakin hedikwatar tunawa da wannan shahid mai daraja, a zauren Soura na Hozeh Honari, kuma an bayyana tambarin da taken wannan lokacin. Hoto: Mohammad Vahdati
-
Yahudawa Da Dama Sun Shiga Gaza: "Matakin Farko Na Samar Masu Da Matsugunai " A Yankin
Kimanin mazauna Isra'ila 20 sun shiga Gaza a ranar Alhamis da motocinsu na sirri, sun bawa daruruwan mitco baya daga kan iyaka zuwa wani yanki da suka sanya wa suna "Kufar Kfar Darom," inda suka kafa tutar Isra'ila.
-
Daukar Fansar Amurkawa Kan ISIS; Barazanar Da Suka Ƙirƙira Da Kansu
Yadda Amerika Da Jordan Su Kai Tarayya A Hare-Haren Kan Syria
Rundunar sojin Jordan ta sanar da shigarta kai tsaye da rundunar sojin samanta a cikin wani aikin hadin gwiwa da Amurka kan abin da ta kira "wuraren ISIS" a kudancin Syria.
-
Yemen Tayi Allawadai Da Keta Alfarmar Alkur’ani Da Amurka Ta Yi
'Yan Yemen Sun Yi Allah wadai da Amurka bayan wulakanta Alqur'ani Mai Tsarki
-
Isra'ila Ta Kama Wani Ɗan Ƙasar Rasha Bisa Zargin Leƙen Asiri Ga Iran
Shin Bet da Hukumar Tsaro ta Ma'aikatar Tsaron Isra'ila sun tsare Vitaly Zvyagintsev, mai shekaru 30, bisa zargin hannu a wani bincike na ɓoye a farkon Disamba.
-
Rahoto Cikin Hotuna | Na Jana'izar Shahid Saleh Amani a Tabriz
An yi jana'izar shahidin tafarkin hidima, shahidin mai kashe gobara "Saleh Amani", a safiyar yau Juma'a (19 ga Disamba, 2025) daga hedikwatar sashen kashe gobara ta Tabriz zuwa Saat Square, tare da halartar Al’ummar shahid, shahidan juyin juya hali, da abokan aikin shahidin. Hoto: Masoud Sepehrinia
-
Amurka Ta Sanya Takunkumai Kan Manyan Jiragen Ruwa 29 Da Kamfanonin Iran
Amurka Ta Sanya Takunkumai Kan Manyan Jiragen Ruwa 29 Da Ke Dauke Da Man Fetur Na Iran Da Kamfanonin Gudanarwa.
-
An Gudanar Da Mauludin Iyayen Annabi (S) Karo Na Biyu A Da'irar Katsina + Hotuna
A ranar Laraba 27/Jimada Thani/1447, daidai da 17/Disamba/2025, 'yan uwa na da'irar Katsina, suka gudanar da babban taron Mauludin Iyayen Annabi (S) karo na biyu wanda wasu gungun matasa (mawaƙa) na Fiyayyar Mata (Khadiman Iyayen Annabi (S) ke shiryawa.
-
Labarai Cikin Hotuna | Sheikh Zakzaky Ya Ziyarci Haramin Sayidah Ma'asumah (As)
Sayyid Sheikh Ibrahim Zakzaky {H}, shugaban 'yan Shi'a na Najeriya, ya ziyarci Haramin Sayyidah Fatima Ma'asumah (Alaihassalam) da ke birnin Qom a yammacin yau, Alhamis (18.12.1404).
-
Labarai Cikin Hotuna | Na Taron Gabatar Da Littafin " Runbun Ilimin Shi'a"
Kamfanin Dillancin Labaran ƙasa da ƙasa na Ahlul-Baiti (ABNA) ya habarta cewa: An gudanar da bikin buɗe "Ƙwafi na littafin Runbun Ilimin Shi'a" mai taken "Gabatar da Shi'a a Duniyar Yau; Bukatu da Kalubale" a yau, Alhamis, 18 ga Disamba, 2025 a zauren taro na Majalisar Duniya ta Ahlul Bayt (AS).
-
Tsarin Ilimi Don Gabatar Da Shi'a, Bisa Ga Hankali Da Fahimtar Ɗan Adam
An Gudanar Da Bikin Buɗe Babban Littafi Na "Runbun Ilimin Shi'a"
A wani biki da aka gudanar a yau, Alhamis, 18 ga Disamba, 2025, a zauren taro na Majalisar Duniya ta Ahlul Bayt (AS) da ke Qom, an bayyana "Ƙwafi Runbun Ilimin Shi'a".
-
Jakadun Amurka, Saudiyya, Da Faransa Sun Gana Da Kwamandan Sojojin Lebanon
Jakadun musamman na Amurka, Saudiyya, da Faransa zuwa Lebanon sun fitar da wata sanarwa daga Paris a ranar 18 ga Disamba, 2026, inda suka sanar da ganawarsu da Kwamandan Sojojin Lebanon, Manjo Janar Rodolphe Heikel, don tattauna ci gaban "Shirin Garkuwar Kasa".
-
Majalisar Wakilan Amurka Ta Ki Amincewa Da Takunkumin Soji Akan Venezuela
Trump: Ba Za Mu Bar Kowa Ya Karya Dokar Hana Shigowa Da Fita Daga Venezuela Ba
Donald Trump ya yi ikirarin a cikin wata sanarwa cewa Venezuela ta "Mallake" albarkatun mai da makamashi na Amurka kuma ya jaddada cewa gwamnatinsa tana da niyyar kwace dukkan wadannan albarkatu; sa'o'i bayan haka, Majalisar Wakilai ta Amurka ta kada kuri'a kan kudirin hana daukar matakin soja kan Venezuela, wanda hakan bai haifar da wani cikas ga qudirin da Washington ke aikatawa ga Venezuela ba.
-
Rahoto Cikin Hotuna Na | Yadda Aka Karrama Manyan Masu Yaɗa Koyarwar Imam Khumaini Qs Na Duniya
Jagoran Harkar Musulunci Sheikh Ibraheem Yakoub Zakzaky (H) ne ɗaya daga cikin na fari a karramawar.
-
An Gano Wasu Ƙabarin Bai Ɗaya A Wani Tsohon Hedikwatar Tsaro
Siriya: An Kama Wata Tawagar ISIS A Idlib
Ma'aikatar Harkokin Cikin Gida ta Siriya ta sanar da kama wata kungiyar 'yan ta'adda ta ISIS mai mambobi 8 a lardin Idlib a arewacin kasar.
-
Hizbullah: Tayi Bankwana Da Wasu Gungun Shahidanta + Bidiyo
Yadda aka gudanar da bankwana ga shahidan gwagwarmayar Musulunci.
-
Yadda Aka Gudanar Da Taron Mauludin Sayyidah Zahra As Katsina + Hotuna
Wasu daga cikin hotunan yadda taron Mauludin Sayyida Fatima (S.A) wanda 'yan uwa na da'irar Katsina suka gabatar a ranar Litinin 24/Jimada Thani, dai dai da 15/Disamba/2025, a muhallin Markaz.
-
Morocco Ta Ƙaddamar Da Masana'antar Samar Jiragen Yaƙi Marasa Matuƙa Na Isra'ila
Morocco ta fara samar da jiragen yaƙi marasa matuƙa na Isra'ila kusa da Casablanca a matsayin wani ɓangare na ƙarfafa sojojinta.
-
Iran: IAEA Ba Za Ta Taba Samun Damar Ganin Nukiliyarta Ba
Ministan Harkokin Waje na Iran: IAEA ba za ta sami izinin duba wuraren da suka lalace ba