-
Malama Zeinat: Addinin Musulunci Zai Tabbata A Najeriya Masu Ikon Duniya Ba Za Su Iya Hana Hakan Ba
An gudanar da wani taron na tunawa da ranar shahadar Sayyida Fatima Zahra (A.S) a Tehran a ranar Litinin, wanda ya kunshi jawabi mai muhimmanci daga Malama Zeinatudden Ibrahim, matar Sheikh Ibrahim Zakzaky - shugaban Harkar Musulunci a Najeriya.
-
Labarai Cikin Hotuna: An Kaddamar Da Aikin "Barguna Ga Falasdinu" A Masallacin Claremont Da Ke Cape Town
An gayyaci mahalarta su dinka murabba'ai 15cm x 15cm a launukan Falasdinu. Kowane murabba'i yana wakiltar yara goma da aka kashe a kisan kare dangi da ake ci gaba da yi a Gaza. Manufar wannan aiki ita ce a dinka murabba'ai 2,000, wanda ke wakiltar yara sama da 20,000 waɗanda aka ɓatar da rayukansu. Za a buɗe bargon Falasdinu da aka kammala a Ranar Nuna Goyon Baya ta Duniya ga Al'ummar Falasdinu, 29 ga Nuwamba, 2025.
-
Shugabannin Shi'a Sun Taru Don Tattaunawa Kan Zaɓen Firayim Ministan Iraki
An gudanar da taron "Shugabanin Tuntuba" na ƙungiyoyin Shi'a na Iraki a gidan Haider al-Abadi, tare da halartar Firayim Minista Muhammad al-Sudaani.
-
Bin Salman Zai Sanya Hannu Kan Yarjejeniyar Nukiliya A Tafiyarsa Zuwa Washington
Yariman Saudiyya mai jiran gado zai sanya hannu kan "Yarjejeniyar Tsarin Haɗin Kan Makamashin Nukiliya na zaman lafiya" a lokacin ziyararsa ta aiki a Amurka tare da Shugaban Amurka Donald Trump.
-
Labarai Cikin Hotuna: Koyar Da Littafin 'Arba'una Hadith' A Hussainiya Sheikh Zakzaky Da Ke Jos, Najeriya
A Hussainiya Sheikh Zakzaky da ke Jos, Sheikh Muhammad Auwal Abubakar ya gabatar da darasin Lahadi na mako-mako. Zaman na wannan makon ya mayar da hankali ne kan illolin Riya (bayyana aiki a cikin ibada) a cikin littafin Arba'una na Imam Khomeini Qs.
-
Riyadh: Shugaban Iran Ya Aikewa Da Yarima Saudiyya Saƙon Wasika
Hukumar Yaɗa Labarai ta Saudiyya ta sanar da cewa Yarima Mai Jiran Gado Na ƙasar ya karɓi saƙon rubutu daga Shugaban Iran.
-
Jam'iyyar RDC Iraqi Ta Lashe Zaɓen 2025 A Iraq
Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Iraki ta sanar da sakamakon ƙarshe na zaɓen 'yan majalisar dokoki na shida da aka gudanar a ƙasar.
-
Mahajjatan Indiya Sama Da 42 Ne Suka Mutu A Hatsarin Mota A Saudiyya
Gidan talabijin Indiya Today ya ruwaito a yau Litinin cewa akalla mahajjatan Musulmin Indiya 42 daga Hyderabad sun mutu a hatsarin mota a Saudiyya.
-
Isra'ila Ta Na Shiri Tsaf Domin Yaƙar Lebanon
Wannan rahoton ya zo ne yayin da Babban Hafsan Sojin Isra'ila, Eyal Zamir, ya sake yin kalamai masu tayar da hankali da tayar da jijiyar wuya game da yaƙi da Gaza.
-
An Kama Wani Malami Ɗan Kasar Senegal A Amurka
Kama Imam El-Hadji Hadi Toub, shugaban 'yan asalin ƙasar Senegal na al'ummar Musulmin Yammacin Afirka a birnin New York, ya haifar da damuwa da kuma ƙoƙari da neman a sako shi da masu fafutukar kare haƙƙin baƙi.
-
Sheikh Naim Qassem: Hizbullah Ita Ce Mai Kare Haƙƙin Lebanon
Sheikh Naim Qassem: Hizbullah Ita Ce Mai Kare Haƙƙin Lebanon
A bikin cika shekaru ɗaya da shahadar Hajj Muhammad Afif, Sheikh Naim Qassem, Sakatare Janar na Hizbullah a Lebanon, ya bayyana shi a matsayin shahararren a fagen kafofin watsa labarai da al'adun gwagwarmaya.
-
Daruruwan Fursunonin Gaza Na Ci Gaba Da Shahada A Gidajen Yarin Isra'ila
Likitoci kare haƙƙin ɗan adam sun yi gargaɗin cewa ainihin adadin mutuwar Falasdinawa a gidajen yarin Isra'ila na iya zama mafi girma saboda ɗaruruwan fursunonin da suka ɓace daga Gaza.
-
Ƙasashen Yammacin Duniya Za Su Kirkiro Sabbin Ka'idoji Don Sa’idon Masu Kula IAEA A Iran
Kafar yada labarai ta Amurka Bloomberg ta ruwaito cewa kasashen Yamma na shirin samar da sabbin ka'idoji don sa ido kan masu kula da su a Iran a taron da za a yi na Hukumar Makamashin Nukiliya ta Duniya; batun da ya shafi matsayin ma'ajiyar uranium da aka inganta bayan hare-haren jiragen sama na Amurka da Isra’ila.
-
Makomar Yammacin Asiya Anan Gaba A Binda Ya Faru Iran Da Siriya Zai Iya Faruwa A Iraqi
Iraƙi ita ce sansanin soja na ƙarshe kuma mafi mahimmanci ga Tehran, sai dai idan Tehran ta yi abin da ya saba wa dabarunta na tsaro na shekaru biyu da suka gabata ya zamo sabon yaƙi ya faru a Iraki da Siriya. Yayin da rikicin yankin ke ci gaba da ƙaruwa, masu sharhi sun yi gargaɗin cewa matakin da Amurka da Iran za su ɗauka a Iraki da Siriya na iya canza makomar tsaro da siyasa a Gabas ta Tsakiya.
-
Wannan Lokacin Tarihi Zai Iya Canza Yanayin Tsarin Duniya Da Falasɗinu Na Gaba
Wannan lokacin na "canzawar tarihi ne." Raguwar ikon mallakar ƙasashen yamma, farkawar ra'ayin jama'a, da kuma rawar da ƙasashe masu tasowa ke takawa na iya sake zana makomar tsarin duniya da makomar Falasɗinu. Gwagwarmayar Falasɗinu ba wai kawai wani labari ne na tarihi ba, sai dai ta samar da misali ga ƙasashe da ƙungiyoyi a duniya da ke wajen ikon mallakar ƙasashen yamma don yin tsayayya da tsarin jari-hujja, mulkin mallaka, da mulkin kama karya.
-
Iran Ta Dakatar Da Jirgin Ruwan Dakon Mai A Mashigin Hormuz
Rundunar Sojin Ruwan Iran Ta Kama Wani jirgin ruwan dakon Mai Dauke Da Tan 30,000 Na Man Fetur A Mashigin Hormuz.
-
Rahoto Cikin Hotuna | Baje Kolin Makaman Rundunar Sojin Sama Ta Iran
Rahoto Cikin Hotuna | Baje Kolin Makaman Rundunar Sojin Sama Ta Iran
-
Amurka Ta Gwajin Bam Ɗin Nukiliya Na B61-12 Da Jirgin Yaƙin F-35
Amurka ta yi nasarar gwada bam ɗin nukiliya na B61-12 maras makami a tsakiyar lokacin rani, kamar yadda wata sanarwa daga Sandia National Laboratories ta nuna.
-
Tantuna Da Dama Sun Nutse A Khan Yunis Sanadiyyar Mamakon Ruwan Sama
Hukumar Agaji da Ceto ta Falasdinu ta sanar a yau Asabar cewa tantuna da dama mallakar mutanen da suka rasa matsuguninsu a yankin Al-Mawasi, yammacin birnin Khan Yunis da ke kudancin Zirin Gaza ruwan sama mai ƙarfi ya mamaye su.
-
Isra’ila Ta Kai Manyan Kayan Yaki Kan Iyakar Lebanon
Yayin da gwamnatin Sihiyona ke ci gaba da kai hare-haren wuce gona da iri kan Lebanon, kafofin watsa labaran gwamnatin sun wallafa hotunan mika kayan aikin soja da tankunan sojoji zuwa iyakar Lebanon.
-
Rahoton Cikin Bidiyo | Na Irin Ƙarfin Makamai Masu Linzami Na Iran
Kamfanin dillancin labaran kasa da kasa na AhlulBaiti (As) –ABNA-ya kawo maku wani rahoto kan ƙarfin makami mai linzami masu ci gaba na Iran.
-
WFP Ta Bukaci Karin Taimako Ga Gaza A Yayin Da Isra’ila Ke Cigaba Da Keta Dokar Tsagaita Wuta
Shirin Abinci na Duniya na Majalisar Dinkin Duniya ya yi kira da a kara tallafin jin kai ga Gaza da kuma kare yarjejeniyar tsagaita wuta. A watan Oktoba, mutane 200,000 sun sami tallafin kudi na dijital wanda da sune mutane miliyan daya suka sami tallafin abinci. Duk da yarjejeniyar tsagaita wuta amma ci gaba da take hakkin Falasdinawa da Isra'ila ke ci gaba da yi na kawo cikas ga kokarin murmurewa.
-
Burtaniya Na Ci Gaba Da Aika Jirgin F-35 Zuwa Isra'ila Duk Da Ikrarin Kisan Kiyashi A Gaza
Kotun Burtaniya ta yi watsi da karar da Al-Haq ta shigar tana kalubalantar fitar da sassan F-35 na Birtaniya zuwa Isra'ila a lokacin da ake zargin kisan kare dangi a Gaza. Kotun ta yanke hukuncin cewa irin wadannan hukunce-hukuncen suna karkashin ikon gwamnati ne, ba sa karkashin binciken shari'a.
-
Shugaban Afirka Ta Kudu: Rashin Halartar Amurka Taron G20 Ya Nuna Shan Kayenta
Dangane da barazanar da shugaban Amurka Donald Trump ya yi cewa jami'an kasarsa ba za su halarci taron G20 da za a yi a Johannesburg ba, takwaransa na Afirka ta Kudu Cyril Ramaphosa ya ce hakan shanke ne ga Amurkawa.
-
IRGC: Ta Bankaɗo Tare Da Rusa Cibiyar Ƙungiyar Leƙen Asirin Amurka Da Isra'ila
Wannan muna sanar da mutanen Iran masu daraja cewa, ta hanyar matakan da Ƙungiyar Leƙen Asiri ta Rundunar Tsaron Juyin Juya Halin ta ɗauka, an gano wata cibiyar tsaro da jami'an leƙen Asiri na Amurka da Isra'ila ke jagoranta a cikin ƙasar an kuma wargaza ta bayan wasu lokutan sa ido, bibiya, da sauran matakan leƙen Asiri.
-
Bidiyon Yadda Aka Gudanar Da Ranar Shahidai Labanon
Rahoton daga wajen gagarumin taron bikin "Ranar Shahidai" a Beirut
-
Ikirarin Trump Na Kaiwa Iran Hari Shaida Ce A Hukumce Akan Take Dokar Majalisar Dinkin Duniya
Dr. Ali Matar, farfesa a fannin ilimin siyasa kuma mai bincike kan hulɗar ƙasa da ƙasa da dokokin ƙasa da ƙasa a Jami'ar Lebanon, ya jaddada cewa ikirarin Trump na shiga yaƙi da Iran shaida ce a hukumce game da cin zarafi da keta Yarjejeniyar Majalisar Dinkin Duniya.
-
An Saki Hanibal Gaddafi Daga Gidan Yarin Lebanon Kan Beli Na Dala $900,000
Hukumomin Lebanon sun sanar da cewa an saki Hannibal Gaddafi daga gidan yari bayan ya bayar da beli na dala $900,000.
-
Mutane 9 Sun Mutu Sanadiyyar Tashin Bom A Delhi Inadiya
Aƙalla mutane 9 sun rasa rayukansu bayan fashewar wani abu kusa da tashar jirgin ƙasa ta Lal Qala a babban birnin Indiya. Ba a tantance yanayi na fashewar ba tukuna.
-
A Yau Za’a Fara Zaɓen 'Yan Majalisar Dokokin Iraki Zagaye Na Biyu
Za a gudanar da zagaye na biyu kuma na ƙarshe na zaɓen 'yan majalisar dokokin Iraki daga ƙarfe 8 na safe a yau.