-
Sudan: Birni El Fasher, Da Yaki Ya Lalata, Inda 'Ya'yansa Maza Suka Rubuta Jarumtaka A Jini
Gwamnan Darfur Minni Arko Minawi ya bayyana El Fasher a matsayin birnin da ya canza daga babban birnin zaman lafiya da mutunci zuwa kango cike da barna da kisan kiyashi cike da tashin hankali da rushewar kayayyakin more rayuwa na farar hula.
-
Yemen Ta Gargaɗi Isra’ila: Duk Wani Sabon Hari Da Zata Kai Gaza Za Ta Fuskanci Martani Mai Tsanani
A cikin wani sako, Kwamandan Sojojin Yemen ya yi gargadin cewa idan gwamnatin Sahayoniya ta sake kai wani hari a yankin Gaza, ayyukan sojojin Yemen za su kai ga yankunan da aka mamaye.
-
Hukumar Zaɓen Iraki: Kashi 82% Ne Suka Kaɗa Ƙuri'a A Zaɓen Musamman.
Shugaban Hukumar Kwamishinoni, Omar Ahmed, ya tabbatar a yayin wani taron manema labarai cewa an gudanar da zaɓen musamman cikin nasara da kwanciyar hankali, ba tare da an bayar da rahoton keta haddi ko kuma gazawar fasaha a cikin na'urorin lantarki ba. Ya lyi ishara da cewa Hukumar ta ci gaba da nuna rashin banbanci da rashin nuna son kai ga dukkan 'yan takara.
-
Ta Yi Kira Ga Masu Shiga Tsakani Da Su Kare Tsagaita Wuta
Hamas: Babu Saranda A Kamus Din Gwagwarmayarmu
A karkashin shawarar Masar, kimanin mayaka 200 za su mika makamansu ga hukumomin Masar don a yi musu izinin wucewa zuwa wasu yankuna na zirin Gaza lafiya, a cewar majiyoyin sulhu. An ruwaito cewa yarjejeniyar ta kunshi samar da bayanai game da hanyoyin sadarwa na karkashin kasa a Rafah don lalata su.
-
Labanon: Mutane 28 Su Kai Shahada A Lebanon A Hare-Haren Isra'ila
Ministan Lafiya na Lebanon ya sanar da shahadar mutane 28 a cikin watan da ya gabata sakamakon hare-haren sama na Isra'ila a kasar.
-
Rahoto Cikin Hotuna / Babban Taron Makokin Sayyidah Fatimah Zahra (As) A Basra
Kamfanin Dillancin Labaran ƙasa da ƙasa na na Ahlul Baiti (AS) – ABNA– ya habarto cewa: dubban mazauna Basra sun halarci jana'izar girmamawa da jajantawa ga shahadar sayyidah Fatimah Zahra (amincin Allah ya tabbata a gare ta) a Basra.
-
Ilimin Mata Wajibi Ne Daga Mahangar Musulunci
Hijabi, Alama Ce Ta Tsarki Da Biyayya Ga Sayyidah Zahra (AS)
Sakataren Majalisar Ahlul Bayt (AS), ta duniya a wani taro da ya yi da masu wa'azin tabligi da mata masu kokirin a makarantun hauza na Rasha ya jaddada bukatar fahimtar Musulunci gaba daya kuma ya dauki nauyin da ya hau kan mata Musulmai a wannna zamani shi ne su kasance dauke da makamai guda biyu na "Ilimi da Imani." Tare da yin raddi ga ra'ayoyi biyu masu tsauri masu bin al'ada da yada alfasha, ya dauki ilimin mata a matsayin wajibi kuma ya bayyana hijabi a matsayin muhimmiyar alama da ke nuna matan Musulmai a cikin al'ummar Rasha.
-
Yemen Ta Kama Wata Babbar Cibiyar Leƙen Asirin Isra’ila Da Amurka Da Saudiyya
Yemen ta ƙara da cewa: "Wannan cibiyar tana da alaƙa da ɗakin ayyukan haɗin gwiwa tsakanin hukumomin leƙen asiri na Amurka da Isra'ila da hukumar leƙen asiri ta Saudiyya. Hedikwatar cibiyar tana cikin yankin Saudiyya".
-
Hizbullah Ta Shirye Tsaf Don Fuskantar Duk Wani Hari Na Isra'ila
Makamai masu linzami 7,500 masu ingancin da tabbacin kaiwa ga hadafi a shirye suke domin habarwa.
-
Rahoto Cikin Hotuna | Na Gudanar Da Zaman Makokin Shahadar Sayyida Fatima Zahra (AS) A Kaduna Najeriya
Kamfanin dillancin labaran kasa da kasa na AhlulBaiti (As) –ABNA-ya habarta cewa: bisa raya munasabar Kwanakin Fatimiyya ‘yan uwa musulmi 'yan Shi'a da masoya Ahlul Bayt (AS) a birnin Kadunan Najeriya sun yi taron jajantawa na tunawa shahadar shugabar matayen duniya da lahira Sayyidah Fadimah Siddiqah Tahirah (AS).
-
Labarai Cikin Hotuna | Na Gudanar Da Zaman Makokin Shahadar Sayyida Fatima Zahra (AS) A Kano Najeriya
Kamfanin dillancin labaran kasa da kasa na AhlulBaiti (As) –ABNA-ya habarta cewa: bisa raya munasabar Kwanakin Fatimiyya ‘yan uwa musulmi 'yan Shi'a da masoya Ahlul Bayt (AS) a birnin Kano, Najeriya sun yi taron jajantawa na tunawa shahadar shugabar matayen duniya da lahira Sayyidah Fadimah Siddiqah Tahirah (AS).
-
Hizbullah Ta Yi Kira Ga Gwamnatin Lebanon Da Ta Dauki Tsauraran Matakai Kan Hare-Haren Isra’ila
Da yake magana kan sakon Hizbullah ga manyan jami'ai a kasar, dan majalisar Lebanon ya yi gargadi kan kokarin Amurka da gwamnatin Sahyoniya na jawo Lebanon cikin tarkon siyasa da diflomasiyya, sannan ya yi kira ga gwamnati da ta dauki tsauraran matakai.
-
Amurka Na Shirin Kafa Sansanin Soja A Sansanin Sojin Sama Da Ke Damascus.
Shirin da Amurka ba ta bayar da rahoto a baya ba na kafa sansanin soja a babban birnin Siriya na nuna cewa an sake daidaita dangantakar da ke tsakanin Siriya da Amurka bayan faduwar tsohon shugaban kasar Siriya Bashar al-Assad a bara.
-
Isra’ila Na Ci Gaba Da Kai Hari Ta Sama Da Kasa A Kudancin Lebanon.
Jiragen yaƙin Isra'ila sun kai hare-hare kan garuruwa da dama a kudancin Lebanon.
-
Yaduwar ‘Yan Ta’addan Al-Qaeda A Afirka Tun Daga Mali Zuwa Najeriya
Ƙungiyar Nusratul-Islam wal-Muslimeen - reshen al-Qaeda a Sahel - an kafa ta ne daga rassan cikin gida da dama a Mali, kuma a yau, ta hanyar hauhawar tashin hankali da shugabanci mai kama da juna, ta zama ɗaya daga cikin ƙungiyoyin da suka fi tasiri a yankin.
-
Jagora (H) Ya Gabatar Da Zaman Juyayin Shahadar Sayyidah Zahra (SA) + Hatuna
Da yammacin Laraba 14 ga Jimadal Ula, 1447 (daidai da 5/11/2025) ne Jagoran Harkar Musulunci, Shaikh Ibraheem Zakzaky (H) ya gabatar da jawabin tunawa da Shahadar Sayyida Fatima Azzahra (SA), a gidansa da ke Abuja.
-
Me Rundunar Sojin Ƙasashen Duniya Ke Yi a Gaza Ba Da Kariya Ko Kammala Kisan Kare Dangi A Yunƙurin Ƙasashen Duniya?
Takardar ta bayyana cewa rundunar kasa da kasa za ta kasance tana da alhakin kare iyakokin Gaza da Isra'ila da Masar, kare fararen hula da hanyoyin jin kai, kuma ayyukanta sun hada da lalata da hana sake gina kayayyakin more rayuwa na soja, da kuma kwace makamai da horar da rundunar 'yan sandan Falasdinu wadda za ta hada kai da rundunar kasa da kasa a cikin aikinta.
-
Mayakan Hizbullah Biyar Ne Su Kai Shahada A Hare-Haren Isra'ila
Sojojin Isra'ila sun kai hare-hare ta sama a yankin Nabatiyeh da Kafr Rumman a kudancin Lebanon. Sun kashe mayaka biyar na Hizbullah, ciki har da wasu daga cikin rukunin Rizwan na musamman An ce ɗaya daga cikin mayakan yana gyara cibiyoyin tsaro lokacin da aka kai hari.
-
Dawowar Sojojin Isra'ila Daga Gaza Kamar Shiga Wata Jahannama Ne
A cewar Le Figaro, da yawa daga cikin sojojin Isra'ila da suka dawo daga Gaza suna fama da mummunan rauni—na jiki da na rai da ruhi. Wahalarsu ba ta ƙare a dakatar da yaƙin ba; tana ci gaba a rayuwarsu ta kashin kansu. Da yawa ba za su iya komawa rayuwa ta yau da kullun ba kuma suna fama da matsalar damuwa bayan tashin hankali (PTSD).
-
Kiristocin Najeriya Da Musulmai Sun Yi Allah Wadai Da Barazanar Soja Ta Trump
Kungiyoyin addinai na Najeriya sun nuna adawarsu ga barazanar Donald Trump na yiwuwar shiga tsakani na soja don mayar da martani ga kisan Kiristoci a kasar.
-
Kwamandan CENTCOM Ya Gana Da Firayim Ministan Da Ministan Tsaron Qatar
Kwamandan Rundunar Sojojin Amurka (CENTCOM) ya yi tafiya zuwa Qatar inda ya gana da kuma yin tattaunawa daban-daban da Firayim Ministan kasar da Ministan Tsaro.
-
Labarai Cikin Hotuna | Shekh Zakzaky H Ya Gana Da Manyan Malamai A Abuja
Yunƙurin haɗin Kan Malaman addinin Musulunci, Prof. Ibraheem Maqari da tawagarshi sun ziyarci Jagora Sheikh Ibraheem Zakzaky (H) jiya Lahadi a gidansa dake Abuja. Bayan gabatar da jawabai da shawarwari akan muhimmancin haɗin kai da kusantar juna tsakanin malaman addini, Jagora (H) ya ƙarfafi wannan ƙoƙari sannan yayi fatan alkhairi da samun nasara. Szakzakyoffice 02/11/2025
-
Sheikh Zakzaky: Isra'ila Na Amfani Da Matakin Tsagaita Wuta Ne A Matsayin Yaudara Kawai
Sheikh Ibrahim Zakzaky, shugaban Harkar Musulunci a Najeriya, ya soki gwamnatin Isra'ila saboda daukar yarjejeniyar tsagaita wuta a matsayin mara ma'ana, yana mai tabbatar da cewa ba za ta taba aiwatar da yarjejeniyar zaman lafiya da Lebanon ko Gaza ba.
-
Jami'in IRGC Ya Yi Shahada A Harin Ta'addanci A Sistan Da Baluchestan
Wani sojan rundunar kare juyin juya halin Musulunci (IRGC) ya yi Shahada a wani harin ta'addanci a lardin Sistan da Baluchestan da ke kudu maso gabashin Iran.
-
Labarai Cikin Hotuna | Yadda Aka Lullube Haramin Sayyidah Ma’asumah As Da Bakaken Banoni A Lokacin Shahadar Sayyidah Fadimah As
Labarai Cikin Hotuna | Yadda Aka Lullube Haramin Sayyidah Ma’asumah As Da Bakaken Banoni A Lokacin Shahadar Sayyidah Fadimah As
-
Pakistan Ta Kori 'Yan Gudun Hijira Sama Da 15,000 Na Afghanistan
A cewar jami'an Afghanistan, Pakistan ta kori 'yan gudun hijira sama da 15,000 na Afghanistan ta hanyoyin kan iyaka guda uku.
-
Kungiyoyin Falasdinawa Sun Yi Alƙawarin Yin Tsayin Daka Har Sai An 'Yantar Da Yankunan Da Aka Mamaye.
A ranar 2 ga Nuwamba, 1977, Sakataren Harkokin Wajen Burtaniya na wancan lokacin, Arthur James Balfour, ya fitar da Sanarwar Balfour a cikin wata wasiƙa zuwa ga Lord Rothschild, shugaban ƙungiyar Zionist ta duniya, inda ya bayyana goyon bayan Birtaniya ga kafa Isra'ila a ƙasar Falasdinu.
-
Girgizar Ƙasa Mai Girman Maki 5.6 Ta Girgiza Kabul Da Arewacin Afghanistan
Wata girgizar ƙasa mai ƙarfi da ta kai maki 5.6 a ma'aunin Richter ta girgiza Kabul da wasu lardunan arewacin Afghanistan. Babu wani rahoto game da asarar rayuka ko kuma yiwuwar barna zuwa yanzu.
-
Gudanar Da Darussan Halayya Ga Ɗaliban Shi'a A Husainiyar Rasulul Akram A Najeriya + Hotuna
Sheikh Ismail Yushua yana gudanar da darussa na ɗabi'ar kyawawan halaye da ilimin Musulunci ga ɗaliban Shi'a kowace Juma'a a Husainiyar Rasulul Akram da ke Jihar Kaduna, Najeriya, kuma yana koyar da ƙa'idodin tausayawa, ɗabi'ar halaye, da rayuwa bisa ga koyi da rayuwar Annabi (SAW).
-
Rahoto Cikin Hotuna | Makokin Shahadar Sayyidah Fatimah Zahra (As) A Gundumar Wasit, Iraki
Kamfanin Dillancin Labaran ƙasa da ƙasa na na Ahlul Baiti (AS) – ABNA– ya habarto cewa: Mutanen Gundumar Wasit sun yi taron makokin karo na 18 don tunawa da shahadar Sayyidah Fatimah Zahra, Shugabar matayen duniya da lahira.