7 Janairu 2026 - 20:10
Source: ABNA24
Isra’ila Ta Kai Hari Kudancin Lebonan

Gwamnatin Isra'ila ta kai hari kan wata mota a wajen birnin Joya, kudancin Lebanon, inda ta yi sanadin shahadar mutum daya da raunata wani dayan.

Kamfanin Dillancin Labaran ƙasa da ƙasa na Ahlul-Baiti (ABNA) ya habarta cewa: Ma'aikatar Lafiya ta Lebanon ta sanar da cewa mutum daya ya yi shahada, wani kuma ya ji rauni a wani hari da jiragen saman Isra'ila marasa matuki suka kai kan wata mota a yankin Joya da ke kudancin Lebanon a yau din nan.

Sojojin Isra'ila, suna ci gaba da karya yarjejeniyar tsagaita wuta, sun kai hari kan yankin da ke kewaye da garin Dirmimas a kudancin Lebanon da manyan bindigogi.

Ra'ayinka

You are replying to: .
captcha