-
Sheikh Ibrahim Zakzaky {H} Ya Gana Da Ƴan Uwa 33 Da Aka Sako Daga Gidan Yari
Da safiyar jiya Alhamis 1 ga watan Zulhijja, 1446 (29/5/2025) ne Jagora Shaikh Ibraheem Zakzaky, ya gana da ragowar ‘yan uwa mutum 33 da suka fito daga kurkuku, bayan shafe kimanin shekaru shida suna tsare tun bayan waki’ar 22 ga July 2019 a Abuja.
-
Sheikh Yakubu Yahaya: Hatta Waƙi'ar Buhari Ba Ta Iya Raba Ƴan Uwa Da Jagoranci Ba
Sheikh Yaqoub ya ƙara jaddada cewa, ‘yan uwa a cikin Harka na da manyan hadafi guda biyu: Na farko, mutum ya samu tsira a gaban Allah (SWT) ta hanyar sauke nauyin da aka ɗaura masa. Na biyu kuma, shi ne samun ƙiyadar jagoranci ba tare da rarrabuwa ba koda kuwa an samu bambance-bambancen fahimta ko ra’ayi.
-
Shaikh Zakzaky H Ya Gana Da Ɗaliban Fudiyyah + Hotuna
Jiya laraba 23 ga watan DhulQa'ada, 1446H (21/05/2025) Jagora Shaikh Ibraheem Zakzaky (H), kamar yadda aka saba kowacce shekara ya gana da wasu daga cikin ɗaliban makarantun Fudiyya daban-daban waɗanda suke shirin yin bikin haddar Alkur’ani Mai girma, a gidansa da ke Abuja.
-
Lebnon: Isra’ila Ta Kai Hari Kan Wata Mota Mutun Daya Yayi Shahada
Mamaya na ci gaba da karya yarjejeniyar tsagaita bude wuta a kasar Lebanon daga lokaci zuwa lokaci ta hanyar kai hare-hare tare da kashe 'yan kasar ba tare da hukuma ta dauki wani mataki ba.
-
Fitattun Abubuwan Da Suka Faru A Kisan Kiyashin Da Isra'ila Ke Yi A Gaza A Rana Ta 577
Dakarun mamaya na Isra'ila na ci gaba da kisan kare dangi a zirin Gaza, bayan sun ci gaba kisansu tun kwanaki 49 da suka gabata da kuma kwanaki 577 da fara kai farmakin Guguwar Aqsa. Hakan ya biyo bayan sabawar da Firaminista Benjamin Netanyahu ya yi kan yarjejeniyar tsagaita bude wuta, tare da goyon bayan da Amurka ke yi na siyasa da soji, a yayin da kasashen duniya suka yi shiru da kuma watsin da ba’a taba ganinsa a kasashen duniya ba.