-
Amurka Ta Tura Wasu 'Yan Ci-Ranin Iranawa, Afghanawa, Georgiyawa Da Turkiyawa Zuwa Afirka
Bisa ga bayanan jiragen sama da wani lauyan shige-da-fice, wani jirgin saman Amurka dauke da 'yan ci-rani da aka kora ciki har da 'yan Iran, 'yan Afghanistan, 'yan Georgia da 'yan Turkiyya, ya tashi zuwa Afirka ta Tsakiya, kuma zai tsaya a Ghana. Wannan ya faru ne a daidai lokacin da wadanda aka kora da lauyoyi suka ba da rahoton cin zarafi a Ghana da kuma tsare-tsare ba tare da iyaka ba a Eswatini.
-
Yarjejeniyar Amurka Da Iran Tsakanin Yaudara Da Cin Amana
Tsakanin Kai Harin Bama-bamai Da Tattaunawa; Yadda Jaridun Amurka suka Yi Nazari a Kan Sanarwar Trump Game Da Cimma Yarjejinaya Da Iran. A daidai lokacin da barazanar soji ta Amurka a kan Iran ta kai ga tsororuwar fadada hari, Donald Trump ba zato ba tsammani ya yi maganar cimma yarjejeniya ta siyasa. Wannan canjin, jaridun Amurka sun kimanta shi a matsayin wani muhimmin juyi, amma har yanzu ba a fayyace komai ba game da rikicin Tehran da Washington.
-
Yakin Ya Haifar Da Raguwar Yawan Makamai Masu Linzami Da Matsin Lamba Kan Sojoji
Mujallar Amurka: Yaƙi Da Iran Ya Fallasa Ƙarancin Ƙarfin Dabarun Amurka
Mujallar "Foreign Policy" a cikin wani rahoto na Hal Brands, farfesa a harkokin dangantakar ƙasa da ƙasa na Jami'ar Johns Hopkins, yayin da yake nazarin sakamakon harin da aka kai wa Iran, ya ikrarin cewa wannan rikici ba wai kawai rikicin Gabas ta Tsakiya bane, har ma gwaji ne ga ƙarfin soji da dabaru na Amurka. Wannan rahoto ya jaddada cewa ci gaba da yaƙi ya haifar da yawaitar amfani da kayan yakin Amurka (ciki har da makamai masu linzami na Tomahawk, na'urorin tsaro na THAAD da Patriot) da kuma ƙara matsin lamba kan sojojin ƙasar, kuma sake gina waɗannan kayan yakin gaba ɗaya na iya ɗaukar shekaru.
-
Sojojin Amurka Sun Taimaki Isra’ila Wajen Dakile Makamai Masu Linzami Na Iran
Wani jami'in Amurka wanda ya gwammace a sakaya sunansa da asalinsa, ya ce: "Mun harba makamai masu linzami na dakile hari a lokacin arangama ta baya-bayan nan tsakanin Iran da Isra'ila".
-
Pentagon Ta Share Ƙungiyoyin Akida 180 Daga Jerin Littafinta A Hukumce
Ma'aikatar Yaƙi ta Amurka ta rage adadin addinai da ƙungiyoyin akida da aka amince da su a cikin dakarun ta'adda na Amurka daga kusan 211 zuwa 31.
-
Ilhan Omar: Isra'ila Ta Bayar Da Umarnin Gudanar Da Tsarin Da Tai A Gaza Akan Labanon
‘Yar majalisar dokokin Amurka 'yar Democrat kuma musulma a cikin wani sako ta bayyana cewa Tel Aviv tana aiwatar da tsarin Gaza a Labanon, ba tare da wani kariya ba, kuma ta jaddada taken cewa: "Babu wani taimakon Amurka ga Isra'ila".
-
Amurka: An Samu Harbe-Harbe A Kusa Da Fadar White House
Biyo bayan rahotanni game da faruwar harbin bindiga kusa da Fadar White House, an ajiye jami'an tsaro a kusa da wannan fada, sannan an jibge kwararrun maharba a kan rufin gine-gine.
-
Daftarin Yarjejeniyar Iran Da Amurka Zai Kawo Ƙarshen Yaƙi A Dukkan Fagagen Daga
Jaridar New York Times a bayan sanarwar da shugaban ƙasar Amurka ya yi game da shirya yarjejeniya tsakanin Tehran da Washington da ake jiran kammalawa, ta yi iƙirarin cewa: Daftarin yarjejeniyar tsakanin Iran da Amurka zai haifar da kawo ƙarshen yaƙi a dukkan faɗin fagen yaki.
-
Rubio: An Samu Ci Gaba A Tattaunawar Da Ake Yi Da Iran
Ministan harkokin wajen Amurka ya sanar: A yayin tattaunawar da ake ci gaba da yi da Iran, an samu wasu ci gaba na musamman.
-
Amurka Ta Kira Taliban Da Ta Kawo Ƙarshen "Yin Garkuwa Da Mutane"
Mai ba da shawara kan tsaron ƙasa na Amurka ya soki abin da ya kira "Siyasar yin garkuwa da mutane" na Taliban, inda ya buƙaci a saki 'yan ƙasar da ake tsare da su da kuma kawo ƙarshen wannan siyasar.
-
Kasuwancin Mai Da Tsadarsa Ba Zai Taba Komawa Yadda Ya Ke Ba Kafin Yaƙi
Mujallar Newsweek: Kasuwancin man fetur da iskar gas ba zai taba zamowa iri daya ba bayan yakin Iran.
-
Amurka Ta Fara Tatsar Kawayenta Na Larabawa
Amurka Ta Sanya Hannu Kan Yarjejeniyoyin Sayar Da Makamai Ga Ƙasashen Larabawa Ta Dala Biliyan 25.7
Yaƙin da ake yi yanzu bai zama abin daukar darasi ba ga Larabawa har yanzu suna kara shiga cikin taqaddamar tsaron gizo-gizo.
-
Ria Novosti: Dala Biliyan 70 Haƙiƙanin Asarar Yaƙin Amurka Kan Iran
Hurst, babban jami'in kula da harkokin kudi na Pentagon, ya yi ikirarin cewa kudin yakin da aka yi da Iran ya zuwa yanzu ya kai kusan dala biliyan 25. Wanda kafafe da masu nazari kan yaƙi su ka sha ƙaryata hakan, wasu na cewa ya kai dala biliyan 50 zuwa 70 amma bisa hakika ba za'a iya kiyasta wannan Asarar ba har sai an kawo ƙarshen yaƙin kana.
-
Patricia: Kiyasin Asarar Da Amurka Ta Yi A Ƴaki Da Ya Kai Dala Biliyan 140
Manazarciyar Soji: Karya su ke yi, ainihin asarar kudin yakin ga Amurka ya zuwa yanzu ya kasance tsakanin dala biliyan 120 zuwa dala biliyan 140.
-
Dan Majalisar Amurka: Zama Shugaban Ƙasa A Amurka Yana Buƙatar Yarjejewar Isra'ila
Taylor Green, dan majalisar dokokin Amurka da ya yi murabus daga majalisar, ya ce domin wani ya zama shugaban Amurka, dole ne ya amince da tsarin Isra'ila in ba haka ba ba zai iya damar samun wannan ikon ba.
-
Pentagon Ta Bayyana Adadin Asarar Kuɗin Yaƙi Da Iran
CNN: Kiyasin dala biliyan 25 da wani babban jami'in Pentagon ya bai wa 'yan majalisa na jimillar kudin yaki da Iran abin takaici ne kuma bai hada da kudin gyara barnar da aka yi wa sansanonin Amurka a yankin ba.
-
Rahoto Cikin Hotuna | Na Harbin Bindiga A Liyafar Shekara-Shekara Ta Fadar White House
Kamfanin Dillancin Labaran ƙasa da ƙasa na Ahlul-Baiti (ABNA) ya rahoton cewa: Jami’an Sirrin Amurka, bayan jin karar harbin bindiga a bikin shekara-shekara na 'yan jarida na Fadar White House, sun fitar da Donald Trump, shugaban ƙasar Amurka, daga wajen taron. Wannan lamarin ya faru ne ɗan lokaci bayan karfe 8:30 na dare agogon gabacin Amurka, sakamakon jin karar harbin bindiga, wanda ya sa mahalarta suka gaggauta ficewa daga wurin. Jami'an Sirri ne suka fitar Trump da Melania cikin gaggawa wajen taron.
-
Yadda Akai Harbe-Harben Bindiga A Wurin Liyafar Abincin Dare Na Trump Tare Da 'Yan Jaridar Amurka + Bidiyo
Bayan jin karar harbi a liyafar abincin dare ta 'yan jarida na Fadar White House, an fitar da Donald Trump daga wurin tare da tawagar tsaronsa.
-
Ƙasa Da Shekaru 6 Amurka Ba Zasu Iya Maye Gurbin Harsashen Da Ta Lalata Su A Yaƙi Da Iran Ba
Rahotonnin tsaron Maƙiya sun fitar cewa zai iya ɗaukar har zuwa shekaru shida kafin a maye gurbin dukkan harsasan da aka yi amfani da su a yaƙin da ake yi da Iran.
-
John Filan Ministan Sojojin Ruwan Amurka
Gwamnatin Trump na ci gaba da yiwa manyan ma'aikatan tsaronta murabus.
-
Iran Ta Mallaki Na'urorin Tsaro Na Zamani Da Iya Gano Dukkan Jiregen Yaƙi Da Kakkaɓo Su
Tsaron saman Iran yanzu ba ya amfani da radar ta gargajiya wanda hakan ya bayyana a ayyukan kakkaɓo jiragen Amurka da Isra'ila da sukai yunkurin kawo mata hari.
-
Guardian: Mummunan Kwanakin Trump Suna Gudana, Gwamnatin Amurka Na Gab Da Rugujewa
Trump ya haifar da rarrabuwar kawuna tsakanin magoya bayansa ta hanyar ayyuka kamar fara yaki mara amfani da Iran, haifar da hauhawar farashin kaya da kuma cin zarafin Kiristoci.
-
Bidiyon Yadda Gobarar Ta Kama A California
'Ƴan sa'o'i da suka gabata wata babbar gobara ta kama wani runbu mai murabba'in ƙafa miliyan ɗaya a Ontario, California. Amma wai ‘Yan sandan Amurka sun ce sun kama wanda ya haddasa gobarar.
-
Trump: Na Ci Gaba Da Korar Manyan Hafsoshin Sojin Amurka
Takaddama tana ƙara tsamari tsakanin manyan janar-janar na Amurka kan yakin da Amurka ta ke yi kan Iran inda Sakataren tsaron Amurka ya bukaci Janar Randy George, shugaban ma'aikata, da ya yi murabus kuma ya yi ritaya nan take.
-
CNN: Adadin Sojojin Amurka Da Suka Jikkata Da Mutuwa Ya Kai 290
A ci gaba da yakin da Amurka da Isra'ila ke gudanarwa a kan Iran zuwa yznu adadin wadanda suka rauanta zua mutuwa ya kai 290
-
Bidiyoyin Yadda Gobara Ta Tashi A Matatar Mai A Texas Amurka
Wasu bidiyoyi na gobara ta tashi a wata babbar matatar mai a Texas a matatar Valero da ke tashar jiragen ruwa na Arthur, Texas.
-
Trump Yana Shirin Takaitacen Yaƙi Kan Iran
Wasu jami'ai da ba a bayyana sunayensu ba sun bayyana cewa gwamnatin shugaban Amurka Donald Trump na tunanin yaƙi mai iyaka kan Iran. Manufar yaƙin zai tilasta wa Iran amincewa da yarjejeniyar nukiliya tare da sharuɗɗan Washington.
-
Amurka: An Jibge Sojojin Tarayya A Wasu Birane Biyar Domin Dokar Shige Da Fice Ta Trump
Shugaban Amurka Donald Trump ya sanar da shirin tura sojojin shige da fice na tarayya a sabbin birane biyar a matsayin wani ɓangare na manufarsa ta "faɗaɗa iyakokin yaƙi da hana shige da fice." Ƙungiyoyin masu goyon bayan baƙi suna kallon wannan matakin a matsayin yunƙuri na ƙara matsin lamba ga al'ummomin baƙi da tsoratar da su.
-
Zanga-Zangar Adawa Da Shugabancin Trump Ta Na Ci Gaba Kafin Rufewar Gwamnati
Manufofin shige da fice na gwamnatin Amurka ba su takaita ga kai gwamnatin tarayya rufewa ba, har ma sun haifar da ci gaba da zanga-zangar kan tituna a mako na biyu a jere.
-
An Kai Wa Wakiliya Musulmi Hari Yayin Da Take Sukar Siyasar Trump Ga Masu Hijira A Amurka
An kai wa Ilhan Omar, Musulma 'yar Majalisar Dokokin Amurka a Minnesota, hari da wani ruwa da ba a san komai ba ne ba daga cikin sirinji a wani taron jama'a a Minneapolis, yayin da take cewa ya kamata Kristi Noem, Sakatariyar Tsaron Cikin Gida ta Amurka, ta yi murabus kuma a dauki matakin shari'a a kanta.