A cikin birane da dama na kasar ta Senegal an fara gudanar da kiran a kaurace wa kayan da aka kera a Amurka domin nuna kin amincewa da siyasar kasar.
Masu gudanar da kamfe din suna bijiro da kayan da aka kera a kasar Turkiya a matsayin wadanda za su maye gurbin na Amurka a kasuwannin kasar ta Senegal.
Kasar Amurka ta kakaba wa wasu jami'an kasar Turkiya takunkumi kamar kuma yadda da sanya kudin fito masu yawa akan karafan da kasar take saya daga Turkiya.
Gwamnati da al'ummar kasar Turkiya suna zargin Amurka da kokarin raunana tattalin arzikin kasar tasu