9 Agusta 2026 - 16:19
Source: ABNA24
Amurka Ta Ɗauki Alhakin Gudanar Da Kamfanonin Siminti A Kan Iyakar Gaza

Rediyon sojojin Isra’ila ya ba da rahoton cewa an bawa Amurka hakkin kulawa da samar da kuɗaɗe da gudanar da kamfanonin siminti a kan iyakar Gaza; kamfanonin da aka kafa don samar da kayan da ake amfani da su wajen rufe ramummuka. A lokaci guda, wannan kafar ta yi iƙirarin cewa Benjamin Netanyahu da "Yisrael Katz" sun amince a asirce da fara wani aiki don ƙirƙirar ababen more rayuwa da gina rukunin gidaje na Falasdinawa a gabashin Rafah; iƙirarin da ofishin Netanyahu ya bayyana a matsayin karkatarwa ga abinda yak e faruwa a gaske da yada bayanan da suka shude a baya.

Kamfanin Dillancin Labarai na Ahlul-Bayt (a.s) – ABNA – ya bayar da rahoton cewa: Bisa ga rahoton Rediyon sojojin Isra’ila, an kafa kamfanonin siminti a yankunan "Nahal Oz" da "Karem Shalom" a kan iyakar Gaza a cikin watannin baya-bayan nan, kuma a baya suna aiki da kuɗaɗe da gudanar da ma'aikatar yaƙi na Isra'ila ne.

An kafa waɗannan kamfanonin don samar da simintin da ake amfani da shi wajen rufe ramummuka da sojojin Isra'ila ke ganowa a cikin Gaza, musamman a yankunan da ake kira "layin rawaya."

Dangane da wannan rahoto, za a mayar da alhakin kuɗaɗe da gudanar da waɗannan kamfanonin zuwa cibiyar daidaitawa ta farar hula-soji na Amurka a "Kiryat Gat."

Wannan kafar ta Isra'ila ta bayyana wannan canji a matsayin alamar haɓaka rawar Amurka a hankali wajen gudanar da abubuwan da ke faruwa a Gaza, kuma ta yi tambaya ko za a yi amfani da waɗannan kamfanonin a nan gaba fiye da rufe ramummuka, don wasu manufofi kamar sake gina Gaza.

Har ila yau, rediyon sojojin Isra'ila ya yi iƙirarin cewa Netanyahu da Katz sun amince kimanin makonni biyu da suka gabata, a bayan kafofin watsa labarai, da aiwatar da aikin ababen more rayuwa a yankin da ake kira "Rafah Green" a gabashin Rafah; shirin da bisa ga shi za a gina rukunin gidaje ga Falasdinawa, wanda ba ya ƙarƙashin ikon Hamas, kuma a ƙarƙashin kulawar dakarun ƙasashe da yawa.

Duk da haka, ofishin Netanyahu a martani ga wannan rahoto ya bayyana cewa wannan labari yana karkatar da hanlula ne ga gaskiyar abubuwan da ke faruwa kuma yana sake yada bayanan da suka gabata.

Ofishin Firayim Ministan Isra’ila ya ce abin da aka gabatar, wani aikin gwaji ne na UAE wanda ya fara watanni da yawa da suka gabata a cikin zirin Gaza kusa da "layin rawaya" don ƙirƙirar rukunin tantuna ba tare da ikon Hamas ba. A lokaci guda, rahoton ya nanata cewa duk da sanar da tsagaita wuta daga 10 ga Oktoba 2025, hare-haren Isra'ila a Gaza na ci gaba, kuma bisa ga ƙididdigar da aka bayar a wannan rahoto, Falasdinawa 1,257 suka shahada kuma 4,131 suka jikkata.

……………………….

Alamomi

Ra'ayinka

You are replying to: .
captcha