-
Yaduwar ‘Yan Ta’addan Al-Qaeda A Afirka Tun Daga Mali Zuwa Najeriya
Ƙungiyar Nusratul-Islam wal-Muslimeen - reshen al-Qaeda a Sahel - an kafa ta ne daga rassan cikin gida da dama a Mali, kuma a yau, ta hanyar hauhawar tashin hankali da shugabanci mai kama da juna, ta zama ɗaya daga cikin ƙungiyoyin da suka fi tasiri a yankin.
-
Jagora (H) Ya Gabatar Da Zaman Juyayin Shahadar Sayyidah Zahra (SA) + Hatuna
Da yammacin Laraba 14 ga Jimadal Ula, 1447 (daidai da 5/11/2025) ne Jagoran Harkar Musulunci, Shaikh Ibraheem Zakzaky (H) ya gabatar da jawabin tunawa da Shahadar Sayyida Fatima Azzahra (SA), a gidansa da ke Abuja.
-
Kiristocin Najeriya Da Musulmai Sun Yi Allah Wadai Da Barazanar Soja Ta Trump
Kungiyoyin addinai na Najeriya sun nuna adawarsu ga barazanar Donald Trump na yiwuwar shiga tsakani na soja don mayar da martani ga kisan Kiristoci a kasar.
-
Labarai Cikin Hotuna | Shekh Zakzaky H Ya Gana Da Manyan Malamai A Abuja
Yunƙurin haɗin Kan Malaman addinin Musulunci, Prof. Ibraheem Maqari da tawagarshi sun ziyarci Jagora Sheikh Ibraheem Zakzaky (H) jiya Lahadi a gidansa dake Abuja. Bayan gabatar da jawabai da shawarwari akan muhimmancin haɗin kai da kusantar juna tsakanin malaman addini, Jagora (H) ya ƙarfafi wannan ƙoƙari sannan yayi fatan alkhairi da samun nasara. Szakzakyoffice 02/11/2025
-
Sheikh Zakzaky: Isra'ila Na Amfani Da Matakin Tsagaita Wuta Ne A Matsayin Yaudara Kawai
Sheikh Ibrahim Zakzaky, shugaban Harkar Musulunci a Najeriya, ya soki gwamnatin Isra'ila saboda daukar yarjejeniyar tsagaita wuta a matsayin mara ma'ana, yana mai tabbatar da cewa ba za ta taba aiwatar da yarjejeniyar zaman lafiya da Lebanon ko Gaza ba.
-
Gudanar Da Darussan Halayya Ga Ɗaliban Shi'a A Husainiyar Rasulul Akram A Najeriya + Hotuna
Sheikh Ismail Yushua yana gudanar da darussa na ɗabi'ar kyawawan halaye da ilimin Musulunci ga ɗaliban Shi'a kowace Juma'a a Husainiyar Rasulul Akram da ke Jihar Kaduna, Najeriya, kuma yana koyar da ƙa'idodin tausayawa, ɗabi'ar halaye, da rayuwa bisa ga koyi da rayuwar Annabi (SAW).
-
Sudan: Hare-Haren Rundunar RSF Na Kara Tsamari Da Fadadawa A Kudancin Kordofan
Cibiyar Likitocin Sudan ta sanar da cewa akalla mutane 12 ne suka mutu, wasu da dama kuma suka jikkata a hare-haren da Rundunar Sojin Sama ta Kaiwa Sansanonin 'Yan Gudun Hijira ta kai kwanan nan a Kudancin Kordofan.
-
Sudan: Rundunar (RSF) Ta Kashe Sama Da Mutane 2,000 A Al-Fasher
Majiyoyin sojojin Sudan sun sanar da cewa mayakan sa kai da ke da alaƙa da Hadaddiyar Daular Larabawa da aka fi sani da Rundunar (RSF) sun kashe fararen hula sama da 2,000, ciki har da mata, yara, da tsofaffi, a cikin kwanaki biyu bayan sun karɓe iko da birnin Al-Fasher.
-
Hatsari Jirgin Sama Duka Fasinjojin Sun Mutu A Kenya Ciki Har Da 'Yan Hungary Takwas Da Jamusawa Biyu.
Hukumar Kula da Jiragen Sama ta Kenya ta sanar a ranar Talata cewa wani ƙaramin jirgin sama ya yi hatsari a gundumar Kwale, a kudu maso gabashin ƙasar, inda ya kashe dukkan mutane 11 da ke cikin jirgin. Hadarin ya faru ne a lokacin da jirgin ya tashi daga Diani zuwa Kichwa Tembo.
-
An Kashe Uba Da 'Ya'yansa 5 A Hanyarsu Ta Zuwan Makaranta A Libiya.
An harbe su a kusa da kusa inda aka gano wasu bulet a wurin da aka aikata laifin
-
Mummunan Fashewar Bam A Khartoum, Babban Birnin Sudan
A yayin da ake shirye-shiryen sake bude filin tashi da saukar jiragen sama na Khartoum, babban birnin kasar Sudan, an samu wasu munanan fashe-fashe sakamakon hare-haren da jiragen yaki marasa matuka suka haddasa.
-
Gwamnan Darfur: Harin Da Dakarun RSF Suka Kai Harin El Fasher Na Kisan Kiyashi Ne
Gwamnan Darfur da ke yammacin Sudan ya bayyana hare-haren baya bayan nan da Dakarun Ba da Agajin Gaggawa suka kaddamar kan El Fasher, babban birnin Darfur ta Arewa a matsayin kisan kare dangi.
-
Sheikh H. Jalala: "Wayewar Addinin Musulunci Itace Hanya Kadai Ta Kiyaye Mutuncin Dan Adam"
Sheikh Hamed Jalala a cikin jawabin nasa, ya bukaci al’ummar musulmin duniya musamman matasa da malamai da su yi zurfafa tunani a kan “Wayewar Musulunci” tare da amfani da ita a matsayin ma’auni domin samun ci gaba mai dorewa. Ya jaddada cewa wannan wayewa ta samar da cikakkiyar mafita ga kalubale na zamani – da suka hada da dabi'u, siyasa, tattalin arziki zuwa jin dadin jama'a.
-
Shaikh Zakzaky Yayi Kiran A Hada Kai Wajen Yakar Kabilanci Da Rugujewar Tattalin Arziki
Shaikh Zakzaky ya kira al'uma da su fuskanci wadannan makirce-makirce na raba kan al’umma, yana mai jaddada cewa hanya madaidaiciya ta shawo kan matsalolin da ake fuskanta ita ce mu koma ga Allah da gaske cikin addu’a da tawakkali, da fatan a karshe zaman lafiya da tsaro za su dawo su tabbata.
-
Bankin Duniya Ya Yi Hasashen Ci Gaban Tattalin Arzikin Afirka
Bankin Duniya, a cikin rahotonsa na ‘Africa Pulse’ na watanni shida, ya daga hasashen ci gaban tattalin arzikin kasashen Afirka kudu da hamadar Sahara daga kashi 3.5 cikin 100 a rahoton da ya gabata a watan Afrilu zuwa kashi 3.8 bisa 100, bisa dalilai da suka hada da raguwar hauhawar farashin kayayyaki, daidaita darajar kudin waje, da kara zuba jari a manyan kasashe masu karfin tattalin arzikin yankin kamar Habasha, Najeriya, da Ivory Coast.
-
Labarai Cikin Hotuna| Makon Shahadar Sayyid Ahmad Zakzaky A Abuja Najeriya
Labarai Cikin Hotuna| Makon Shahadar Sayyid Ahmad Zakzaky A Abuja Najeriya
-
Yadda ‘Yan Kasar Maroko Suke Tunawa Da Aikin 7 Oktoba + Bidiyo
Bisa tunawa da cika shekaru biyu da fara gudanar da aikin kai hari mai cike da tarihi na ranar 7 ga watan Oktoba a babban birnin kasar Maroko ya cika da tumbatsar al’umma sun masu jinjinawa ga wanna aiki.
-
Sudan: Ambaliyar Ruwa Ta Khartoum Ta Raba Sama Da Iyalai 1,200 Da Muhallansu
Ambaliyar ruwa a birnin Khartoum ta raba sama da iyalai 1,200 da muhallansu, a daidai lokacin da ake fama da matsalar rashin kayan tallafi na jin kai da kuma munanan illolin yakin da ake fama da shi a Sudan, a cewar wani rahoto da kungiyar kula da ‘yan cirani ta duniya ta fitar.
-
Gagarumin Bukin Bude Makarantar Markazul Al-Mustafa (S) A Tanzaniya + Hotuna
Bude makarantar koyon sana'o'i da koyon addini ta Markaz Al-Mustafa ana daukarsa a matsayin wani muhimmin matakin bunkasa cibiyoyi na Musulunci a kasar Tanzaniya wajen shirya matasan da suka hada ilimin zamani da koyarwar Musulunci.
-
Sudan: Majalisar Sarauta Ta Gana Da Majalisar Shugaban Kasa A Daidai Lokacin Da Ake Kiraye-Kirayen Kawo Karshen Yakin Sudan
A wani ci gaba mai ban mamaki na siyasa, majiyoyin jaridu iri daya na kasar Sudan sun ba da rahoton wata ganawa tsakanin mataimaki a majalisar sarautar kasar Sudan da mataimakin shugaban majalisar shugaban kasar. A cewar majiyoyin, taron ya gudana ne a ranar 13 ga watan Satumba a Nairobi babban birnin kasar Kenya, inda wakilan majalisar mulkin kasar suka gana da shugabannin majalisar shugaban kasa na kawancen kafa kungiyar, matakin da ke nuna an sauya salon tunkarar bangarorin da ke rikici da juna. Wannan mataki dai na nuni da yunkurin sake fasalin dangantakar siyasar cikin gida a daidai lokacin da ake ci gaba da matsin lamba a yankuna da na duniya na kawo karshen yakin da ake yi a kasar.
-
Labarai Cikin Hotuna| Na Ziyarar Babban Shehin Majalisar Shi'a Na Tanzaniya Ga Ziyarci Cibiyoyin Ahlul Baiti Na Kigoma.
Labarai Cikin Hotuna| Na Ziyarar Babban Shehin Majalisar Shi'a Na Tanzaniya Ga Ziyarci Cibiyoyin Ahlul Baiti Na Kigoma.
-
Sudan: Ambaliyar Ruwa A Wad Ramli A Arewacin Khartoum Bahri, An Yi Kira Da A Kwashe Mazauna.
A wani mummunan lamari da ya faru a yankin Wad Ramli da ke arewacin birnin Khartoum Bahri, ruwan kogin Nilu ya ratsa yankin a ranar Talata bayan da wani tudun kasa ta ruguje, lamarin da ya zama wani shinge na dabi'a ga magudanar ruwa.
-
Jaruman Kasashen Afirka Mali Njar Da Burkina Faso
Kasashen Afirka Uku Sun Sanar Da Ficewa Daga Kotun Hukunta Manyan Laifuka Ta Duniya ICC.
Kasashen Burkina Faso, Mali da Nijar da ke yankin yammacin Sahel, sun sanar a cikin wata sanarwar hadin gwiwa da suka fitar cikin gaggawar ficewa daga kotun hukunta manyan laifuka ta kasa da kasa (ICC) da ke birnin Hague, tare da tabbatar da rashin amincewa da hurumin wannan cibiya ta kasa da kasa.
-
Rahoto Cikin Hotuna | Na Ganawar Yan Uwa Da Sheikh Ibrahim Zakzaky
Kamfanin dillancin labaran Ahlulbayt na kasa da kasa (ABNA) ya bayar da rahoton cewa: wasu tawagogin mabiya Shi’a a Najeriya sun gana da Sheikh Ibrahim Zakzaky H a gidansa da ke birnin Abuja.
-
Malamin Burkina Faso: Ya Kamata Duniyar Musulunci Ta Yi Koyi Da Iran Game Da Falasdinu
Wani malami mai nazari a Burkina Faso ya jaddada cewa: Idan dukkanin musulmi kamar Iran suka dauki matakin karshe da yanke shawara (don 'yantar da Falasdinu), to za a cimma wannan buri. Iran abin koyi ce ga dukkan musulmi da 'yantattun mutane a duniya, ya kamata mu yi koyi da ita.
-
Yaman: Man Fetur Ɗin Ƙasashen Larabawa Ne Isra'ila Ke Anfani Da Shi Wajen Jefa Bama-Bamai Kan Al'ummar Gaza.
Sayyid Abdul Malik Badreddin Al-Houthi ya ce: Makiya yahudawan sahyoniya suna amfani da bama-bamai na Amurka, Birtaniya da Jamus, wadanda man fetur din kasashen Larabawa ke samar musu da man fetur, wajen aiwatar da kisan kiyashi a Gaza.
-
Labarai Cikin Hotuna | Yadda Almajiran Sayyid Ibrahim Yaqoub Zakzaky (h) Na Birnin Katsina Suka Gudanar Da Gasar Faretin Girmamawa Ga Manzon Allah (s)
Labarai Cikin Hotuna | Yadda Ƴan'uwa Musulmi Almajiran Sayyid Ibrahim Yaqoub Zakzaky (h) Na Birnin Katsina Suka Gudanar Da Gasar Faretin Girmamawa Ga Manzon Allah (s).
-
Yadda Aka Gudanar Da Bikin Maulidin Annabi Muhammad (SAW) A Arusha Tanzaniya + Hotuna
Yadda Aka Gudanar Da Bikin Maulidin Annabi Muhammad (SAW) A Arusha Tanzaniya + Hotuna
-
Shaikh Zakzaky H: Hadin Kai Umarni Ne Daga Allah, Ku Yi Riko Da Igiyar Allah, Kada Ku Rarraba".
Jagoran Harkar Musulunci a Najeriya (IMN) Allamah Shekh Ibrahim Zakzaky H ne ya gabatar da jawabin rufe taron makon hadin kai a Abuja ranar Laraba Ina a jawabinsa ya yi gargadi akan hare-haren da ake kaiwa kasashen musulunci, tare yin kiran hadin kai.
-
Military Watch: Aljeriya Ita Ce Kawai Ƙasar Larabawa Da Ke Da Karfin Kare Hare-Haren Isra'ila
Hare-haren da Isra’ila ta kai kan Qatar a baya-bayan nan ya haifar da ayar tambaya game da yadda sojojin saman Isra’ila za su iya kutsawa cikin wasu kasashen Larabawa, da kuma karfin da wadannan kasashen ke da shi wajen dakile hare-hare.