19 Janairu 2026 - 21:42
Source: ABNA24
Wakiliyar Majalisar Tsaron MDD A Sudan: Shaidun Taurarin Ɗan Adam Sun Tabbatar Da Ta'asar Da RSF Ta Aikata A El Fasher

Rahotonnin sun kunshi hotunan tauraron dan adam, bidiyo da sauti; an aikata laifukan yaki da laifukan cin zarafin bil'adama a El Fasher.

Kamfanin Dillancin Labaran ƙasa da ƙasa na Ahlul-Baiti (ABNA) ya habarta cewa: Wakiliyar Majalisar Tsaron MDD A Sudan tace Waɗannan laifukan sun faru ne musamman a ƙarshen Oktoba, lokacin da RSF ta mamaye birnin.

Ta ƙara da cewa: Bidiyon da muka yi nazari a kansu sun nuna cewa laifukan sun faru ne a sassa daban-daban na Darfur: kashe-kashe, daure mutanen da ba Larabawa ba, da kuma lalata gonaki da kayayyakin more rayuwa da ƙungiyar ta yi.

Shaidu daga majiyoyi daban-daban sun tabbatar da cewa ƙungiyar ce ke da alhakin waɗannan laifukan.

Hotunan tauraron dan adam sun nuna kaburbura da yawa a yankin.

Muna aiki tare da al'ummomi daban-daban don tattara bayanai da shaidu; ƙungiyoyinmu da abokan hulɗarmu sun ba mu bidiyo da shaidu da yawa.

Hotunan da muke da su suna da ban tsoro ƙwarai.

Your Comment

You are replying to: .
captcha