14 Janairu 2026 - 21:38
Source: ABNA24
Amurka Ta Kai Sabbin Hari A Somaliya

Amurka ta kai sabbin hare-haren kan Somaliya bisa fakewa da zargin "yaki da ta'addanci".

Kamfanin Dillancin Labaran ƙasa da ƙasa na Ahlul-Baiti (ABNA) ya habarta cewa: Sojojin Amurka, tare da hadin gwiwar gwamnatin tarayya ta Somaliya, sun kaddamar da hare-hare ta sama kan 'yan kungiyar Al-Shabab a ranar 12 ga watan Janairu. Bugu da kari ta kai wasu hare-hare ta sama a kan reshen kungiyar Isis ta cikin gida a Somalia a ranar 9 da 11 ga Janairu.

Your Comment

You are replying to: .
captcha