2 Oktoba 2014 - 10:02
Somaliya:Gwamnati Ta Fara Samun Nasara Kan Kungiyar Al-Shabab

Dakarun Sojin kasar Somaliya sun ce suna samun gagarumar nasara ga kungiyar nan ta Ashabab. Hukumomi a arewacin yankin Somaliya mai kwarya-kwaryan 'yancin cin gashin kai Puntland, sun ce sun sake kwace wani muhimmin yankin tsauni daga kungiyar Al Shabaab mai alaka da kungiyar Alka'ida.

Yankin tsauni na Galgala na hannun kungiyar Al Shabaab ne tun tsawon shekaru, inda ya kasance babban sansaninsu a arewacin kasar .

 

Daga nata waje Kungiyar ta Al Shabaab ta ce ana gwabza kazamin fada a yankin tsakanin mayakanta da hadin gwiwar Sojin kasar da na kasashen Afirka  amma dai ta ce har yanzu ita ke da iko da iyakokinta.

 

A kudancin  kasar ta Somaliya ma , hadin gwiwar dakarun tarayyar Afirka da sojojin gwamnatin kasar na ci gaba da dannawa birnin Brava mai gabar teku. ABNA