Kamfanin dillancin labarai na Ahlul-Baiti{a.s} - ABNA - Rikici tsakanin makiyaya da masinta da ya samo asali kan wanda ke da ikon yin amfani da ruwa da wasu filaye a ranar 5 ga watan Decemba a kauyen Kousseri ya tilastawa sama da mutane 30,000 tserewa daga gidajensu ba shiri, zuwa kasar Chadi
Tun a ranar Alhamis da ta gabata ce aka aike da jami’an soji zuwa yankin domin dawo da zaman lafiya, da dakile yi w uwa sake afkuwar rikicin , sai dai har ayanzu a kwai fargaba da ake da ita inda har yanzu kasuwanni da wajejan cin abinci sun kasance a rufe, bayan da aka kona wasu daga cikinsu a lokacin rikicin a kauyen Mousgoum tsakanin masinta dad a kuma yan kabilar shuwa Arab da suka kwashe dubban shekaru suna rayuwa a wajen.
Kimanin yan kasar Kamaru 20,000 yanzu haka suke gudun hijira a kasar Chadi wanda sama da 8500 har yanzu suna nan basu koma gidajensu ba sakamon sake barkewar rikicin.
342/