ABNA24 : Wani rahoton na jaridar Sahara Reporters ya ambaci cewa; harsashin ‘yan sandan ya sami wasu Karin masu Zanga-zanagr biyu.
Mutumin da ya rasa ransa, dalibi ne, yayin da wani kuma yake kwance rai kwakwai, mutum kwakwai.
A jahar Delta da kuma birnin tarayyar Abuja, masu Zanga-zangar kamar rundunar ‘yan sanda ta SARS’ sun gamu da fushin jami’an tsaro duk da cewa an gudanar da Zanga-zangar ne a cikin ruwan sanyi.
Ana zargi wannan rundunar ne dai da cin zarafin ‘yan kasa da ya hada da wulakanta su da kuma kisa a wasu lokutan.
A makon da ya shude ma dai mataimakin shugaban kasar ta Nigeria Osinbanjo ya soki lamirin runudunar saboda kashe wani saurayi da ta yi, tare da fadin cewa; An wayi gari al’ummar Nigeria ba su iya tantance tsakanin ‘yan sanda da kuma ‘yan fashi.
342/