(ABNA24.com) Babu shakka kamar yadda muka sani a ko wacce shekara a irin wannan lokacin jagoran harkar Musulunci a Nigeria Sayyid Ibrahim Zakzaky yana tunatar damu muhimmancin watannin nan uku dake jere watau Rajab, Sha’abn, da kuma Ramadan.
Sannan kuma ya kasance yana tunatar da mu cewa tun daga Rajab ake shirin shiga watan na Ramadan, don haka kada muyi sake a dage da addu’oi da ibada.
Muna rokon Allah Ta’ala ya bamu ikon raya wadan nan watanni kamar yadda yake so.
/129