17 Agusta 2026 - 21:20
Source: ABNA24
Tunawa Da Maulidin Annabi Mai Girma Babbar Matattarar Imani Don Komawa Ga Alkibla

Ina muka kasance daga sakon wannan Annabi Mai Girma? Kuma ina al'umma ta kasance daga shirinta na Alkur'ani? Kuma ina matsayinta yake daga yaƙin gaskiya da ƙarya a lokacin da da yawa daga cikin 'ya'yanta suka yi watsi da asalinsu, suka ƙi ka'idojinsu, har ma karkata ta kai wasu zuwa matakin motsi a ƙarƙashin tutar azzalumi da girman kai na Amurka da Isra'ila, a daidai lokacin da ya kamata su kasance cikin addinin da ya ginu a kan adalci da daidaito da gaskiya.

Kamfanin Dillancin Labarai na Ahlul-Bayt (a.s) – ABNA – Tunawa da Maulidin Annabi Mai Girma yana zuwa ga al'ummar Musulunci, ba a matsayin bikin mai wucewa da za a rufe tarihinsa da ƙarewar ranarsa ba, a'a, a matsayin babban mafakar imani don sake duba gaskiya, kimanta tafiya, da maido da alkibla daidai. Dama ce mai daraja don mu tambayi kanmu cikin gaskiya: Ina matsayinmu yake ga sakon wannan Annabi Mai Girma? Kuma ina matsayin al'umma yake ga shirinta na Alkur'ani? Kuma ina matsayinta take daga yaƙin gaskiya da ƙarya a wani lokacin da dayawa daga cikin 'ya'yanta suka yi watsi da asalinsu, suka ƙi ka'idojinsu, har ma karkata ta kai wasu zuwa matakin motsi a ƙarƙashin tutar azzalumi da girman kai na Amurka da Isra'ila, a daidai lokacin da ya kamata su kasance cikin addinin da ya ginu a kan adalci da daidaito da gaskiya.

Tunawa da Maulidin Annabi: Tushe Don Kimanta Wani Yanayi Mai Cike Da Rikitarwa

Wannan lokaci mai albarka yana zuwa ne a wani mataki mafi haɗari a tarihin al'ummarmu; domin al'umma tana fama da ta’addancin Isra’ila da Amurka da rarrabuwar kawuna mai tsanani, da rikice-rikice masu ƙarfi, da sabani na cikin gida da ke lahanta jikinta, da raunana ƙarfinta, da buɗe kofofinta ga maƙiya da suke dakon hakan, don haka abu na farko da ya kamata mu fara da shi a wannan bita shine gyara a tafarkin al'umma; domin karkatar daga barin bin hanya da manhajar Allah da Manzonsa, duk inda ya kai ga zurfafa, sakamakonsa yana kara girma, kuma asararsa tana ƙaruwa, don haka al'umma ce zata biya alhakin yanayin dabi'u da halayya da koyarwarta, kuma hakan yana bayyana a kan dukkan al'amuran rayuwarta na addini da na duniya.

Kuma domin dawo da hanyar daidai ya zama na gaske ba na zahiri ba, dole ne ya ginu a kan tushe mai ƙarfi wato ƙarfafa asalin Musulunci da tunaninsa daidai wanda zai fara daga tambayoyi kamar haka: Su Wanene mu? Kuma menene tushenmu da dabi'unmu? Kuma menene shirinmu a matsayin al'umma? Kuma menene alamomin wannan shiri? Kuma wanene malaminmu, mai ƙarfafawa, abin koyi, da jagora da ya kamata mu kasance da shi a cikin halin yanzu da gaskiyarmu?

Amsar waɗannan tambayoyi ba abu ne kawai na sha'awa ko na tunani, a'a, wanzanjen wajibi mai dorewa, kuma babu shakka yana ga Manzon Allah Muhammad (SAW), wanda ya zo a matsayin rahama ga duniya, da shiriya da haske mai bayyanawa.

Mabayyaniyar Karkata Da Gazawa Mai Kunyatarwa

Gaskiyar al'umma a yau tana kewaya cikin yanayin nau'ika biyu, dukansu suna ba da gudummawa wajen raunana ta da lalata darajarta:

Nau'i na farko: Waɗanda ba su ji kunyar motsi da yunkuri a ƙarƙashin tutar Amurka da Isra'ila, tutar azzalumi da girman kai, tutar zalunci da ta'addanci, tutar fasadi da laifuffuka, sun ɗauki tutar munafunci da fitina a cikin jikin al'umma, kuma sun gabatar wa Musulunci da Larabawa wani hoto maras kyau wanda ke salwantar da al'umma ga maƙiyanta na gaskiya, kuma ya sa ta zama loma mai sauƙi ga masu kwadayi, kuma wannan matakin na karkata mabayyani yana jan hankalin nau'o'i daga cikin al'umma, waɗanda suka sayar da lahirar su da duniya ta wasu, kuma suka maye gurbin ƙarfi da wulakanci.

Nau'i na biyu: Waɗanda suka zaɓi shiru da zama da ko in kula da ƙin daukar nuauyi, a wani lokaci da al'umma ta shiga masifa, kuma masifa ta girma, kuma zalunci ya ƙaru, kuma gaskiya ta bayyana kamar rana, waɗanda suke tsaye a matsayin 'yan kallo ga masifar 'yan'uwansu, kamar suna cikin al'umma ce da ke cikin addinin da ka'idodinsa suka yarda da shiga cikin sahun azzalumi, ko yarda da zalunci, ko yin watsi da laifi da ta'addanci. A'a! Addinin da muke ciki shi ne addinin daukar nauyi; duk abin da ke ciki yana ƙarfafa wannan nauyin: ka'idojinsa da dabi'unsa da koyarwarsa, kuma yana gabatar da mafi girman abin koyi wajen ɗaukar nauyi da kuma motsa shi, wato Manzon Allah (SAW).

Kuma daga cikin muhimman ginshiƙai na asalinmu da dangantakarmu, akwai imani na gaskiya ga Manzon Allah Muhammad (SAW), imani na yarda da ƙauna, imani na so da shiriya, imani na bi da koyi; imani na waɗanda suke jin girmansa, kuma sun san darajarsa, kuma sun fahimci ni'imar Allah a kansu ta wurinsa.

Ni'ima Mai Girma Ta Manzon Shiriya Mai Ceto

Duniya gaba ɗaya a dukkan sassanta tana rayuwa a cikin duhu mai tsanani; shirka da ƙarya sun mamaye, duhu ya yi yawa, kuma ɗan'adam ya zama fursunonin wahala da ɓata, ba shi da manufa a rayuwa, kuma babu wata manufa ta nasara da yake tafiya zuwa gare ta. Hakikanin yanayin Larabawa da na duniya tana ƙarƙashin nauyin jahiliyya da duhunta mai yawa, da ƙazantattunta, kuma tana tafiya zuwa ƙara: ƙaruwar sharri, da raguwar alheri, da ɓacewar kyakkyawar ɗabi'a, ba tare da wani kulawa mai muhimmanci game da muhimmancin abin da suke ciki ba, da mummuna yanayin da suke kansa.

Idan ba don Allah (SWT) ya aiko rahamarsa da haskensa ba, da ɗan'adam ya ci gaba da zurfafa cikin wannan mawuyacin hali, ba tare da wani mai ceto daga Allah da zai riki hannunsa zuwa ga hanya madaidaiciya ba. Kuma Allah ya ce a cikin littafinsa mai girma: "Waɗanda suka kafirta daga ma’abota Littafi da mushirikai, ba su kasance masu rabuwa da juna ba har sai hujja ta zo musu, Manzo daga Allah yana mai karanta takardu masu tsarki, a cikinsu akwai littattafai masu daraja." [Al-Bayyina: 1-3].

  [البينة: 1-3] {لَمْ يَكُنِ الَّذِينَ كَفَرُوا مِنْ أَهْلِ الْكِتَابِ وَالْمُشْرِكِينَ مُنفَكِّينَ حَتَّى تَأْتِيَهُمُ الْبَيِّنَةُ (1) رَسُولٌ مِّنَ اللَّهِ يَتْلُو صُحُفًا مُّطَهَّرَةً (2) فِيهَا كُتُبٌ قَيِّمَةٌ}.

Ta wurin wannan Manzo da Allah ya yi ni'ima da shi, da wannan shiriya mai daraja da ya zo da ita daga takardu masu tsarki (Alkur'ani mai girma), Allah ya ceto ɗan'adam daga ɓatacciyar hanya, kuma ya cece su daga jahiliyya wadda idan ta ci gaba da girma, da sakamakon ta ne ɗan'adam ya rasa duk wani tasirin ɗan'adamcinsa, kuma ya faɗi ƙasa ga matakin dabbobi, ga bauta wa gumaka na dutse da na itace da na mutum ba tare da Allah ba, kuma ya Allantakar da gumaka, kuma da ƙazantattun jahiliyya da ɓarnarta da lalatarta da muguntarta da rashin tsarinta na ɗabi'a sun mamaye dukkan fannonin rayuwa.

A yau, idan muka dubi matsayi mai ban tausayi da raɗaɗi na gaskiyar al'ummarmu bayan Allah ya cece ta ta wurin Annabinsa da shiriyarsa, za mu iya tunanin yadda zai kasance idan ba a aiko wannan Annabi ba, kuma idan ba wannan addini ya zo ba, kuma idan wannan babban canji bai faru ba. Da al'umma ta kasance a cikin yanayin da ya fita daga ɗan'adamcinsa gaba ɗaya, kuma da mun zama garken dabbobi masu ban tsoro da suka ɓace a cikin dazuzzuka marasa amfani. To, yaya girman ni'imar Allah a kanmu, da jinƙansa a gare mu lokacin da ya cece mu daga makomar da babu makawa Jahannama, kuma ya shirya mana hanyar alheri da ceto wadda — idan muka bi ta kuma muka riƙe ta — za ta kai mu ga Aljannarsa da yardarsa a lahira, kuma mu yi farin ciki da ita a rayuwar duniya…

Alamomi

Ra'ayinka

You are replying to: .
captcha