-
Rahoto Cikin Hotuna | Na Hare-haren Gwamnatin Yahudawa A Gaza Da Yammacin Kogin Jordan
Tare da ci gaba da ayyukan soji na gwamnatin yahudawa a zirin Gaza da Yammacin Kogin Jordan, tabarbarewar jin kan bil'adama a yankunan Falasdinu na ci gaba da ƙaruwa, kuma mazauna waɗannan yankuna suna fama da mafi munin sakamakon yaƙi.
-
Rahoto Cikin Hotuna | Yadda Yadda Wurin Kwana Ke Wahala A Gaza
Yaƙi a zirin Gaza ya kai ga tabarbarwar rashin gidaje zuwa matakin da ba a taɓa yin irinsa ba; fiye da kashi 92% na gidaje Isra’ila ta lalata su ko kuma ta rushe wani yankinsu, kuma iyalai na Falasdinu suna ci gaba da neman wurin kwana don ci gaba da rayuwa a cikin mawuyacin yanayi.
-
Rahoton Amurka: Pentagon Da CENTCOM Suna Boye Bayanan Asarar Yaƙi Da Iran
Wani rahoto na gidan talabijin na ABC News ya bayyana cewa, Ma'aikatar Tsaro ta Amurka (Pentagon) da Cibiyar Rundunar Amurka (CENTCOM) suna gujewa buga kididdigar da aka sabunta game da asarar yaƙi da Iran, a cikin tambayoyi game da daidaiton alkaluman hukuma da aka bayar.
-
Reuters: An Samu Raguwar Dakon Man Fetur Bayan Takunkuman Yamen Akan Saudiyya
Reuters: An Samu Raguwar Ayyukan Dako Da Ɗora Danyen Man Fetur Daga Tashar Jiragen Ruwa Ta Yanbu Na Saudiyya Bayan Sanar Da Takunkumin Yamen A Kan Saudiyya
-
Sojojin Yemen Sun Kai Hari A Kan Jirgin Ruwan Dakon Man Fetur Na Saudiyya Da Tilasta Shi Ja Da Baya
Sojojin Yemen sun sanar da aiwatar da wani aikin soji wanda ya kai hari a kan jirgin ruwan dakon man fetur na Saudiyya "NCC GHAZAL," suna tabbatar da cewa, jirgin ya keta dokar hana zirga-zirgar ruwa da aka sanya wa Saudiyya, kuma ya ƙi amsa kiran gargadi.
-
Cikin Bidiyo | Miliyoyin Maziyarta Arba’een Suna Kwarara Zuwa Karbala Domin Ziyarar Arba'in
Cikin Bidiyo | Miliyoyin Maziyarta Arba’een Suna Kwarara Zuwa Karbala Domin Ziyarar Arba'in
-
Kaitsaye: Sojojin Mamaya Sun Kai Hari Da Bama-bamai A Garuruwa Uku A Kudancin Lebanon
Sojojin Mamaya Sun Kai Hari Da Bama-bamai A Garin Kafr Tibnit A Kudancin Lebanon Sannan Sun Kai Hari Da Bama-bamai A Garin Zutar Al-Sharqiyyah A Kudancin Lebanon. Har wala Yau Sojojin Mamaya Sun Kai Hari Da Bama-bamai A Gefen Garin Al-Qantarah A Kudancin Lebanon
-
Reuters: Oman Ta Gabatar Da Shirin Yanki Ga Iran Don Sarrafa Mashigar Hurmuz Tare
Kamfanin dillancin labarai na Reuters, ya nakalto daga wata majiya a yankin Tekun Farisa rahoton cewa, Oman ta gabatar wa Iran wata shawara, tare da goyon bayan wasu kasashen yankin, don samar da wata hanya ta hadin gwiwa wajen sarrafa mashigar Hurmuz; shirin da bisa gare shi, masu amfani da wannan hanyar ruwa za su biya kuɗin ayyukan jigilar ruwa da yadda suke so.
-
FT: Iran Ta Ƙara Dagula Ma'aunin Amurka Da Isra'ila Ta Hanyar Sake Gina Ƙarfin Makamanta Masu Linzami
Jaridar Ingila Financial Times, a cikin wani rahoto tana mai nuni ga ayyukan Iran a 'yan watannin da suka gabata, ta rubuta cewa, Jamhuriyar Musulunci, duk da hare-hare masu yawa, ta sami nasarar kiyaye ƙarfin makamanta masu linzami, kuma ta hanyar sake gina ƙarfin sojinta cikin sauri, ta ƙara dagula ma'aunin Amurka da gwamnatin yahudawa.
-
Iran: Zamu Rufe Fayil Din Isra’la Na Har Abada
Aref: Sake Farwar Yaƙi Da Yahudawa Yana Nufin Kawo Ƙarshen Su Na Har Abada
-
Ƙungiyoyin Kare Hakkin Dan Adam Sun Yi Allah Wadai Da Korar Ma'aikata 'Yan Shi'a Daga UAE
Ƙungiyar kare hakkin dan adam ta Equidem, da ke Landan, ta sanar da cewa, korar ma'aikata 'yan ci-rani da yawa, musamman 'yan Shi'ar Pakistan, daga Hadaddiyar Daular Larabawa, ta kasance tare da zarge-zarge kamar "ƙirƙirar shari'a bisa ga mazhaba," kamewa ba tare da izini ba, hana biyan albashi, da kuma keta tsarin shari'a; dukkan mutanen da wannan hukuma ta yi hira da su, sun ce, bayan halartar masallacin Shi'a da kuma rubuta bayanan su, an kama su kuma an kore su.
-
Politico: Ganawar Netanyahu Da Trump Musiba Ce Ne Ga 'Yan Kungiyar America First
Ganawar Benjamin Netanyahu da Donald Trump ta haifar da tashin hankali a tsakanin masu ra'ayin mazan jiya na jam'iyyar Republican; domin sun yi imanin cewa Netanyahu, don ceto rayuwarsa ta siyasa, yana ƙoƙarin jawo Amurka cikin tarkon yaƙi da Iran.
-
Iran: Duk Wata Ƙasa Da Ta Yi Amfani Da Dukiyoyin Iran, Ba Za Ta Sami Izinin Wucewa Ta Mashigar Hormuz Ba
Mai magana da yawun hedikwatar Khatamul-Anbiya ya yi gargadin cewa, duk wani kamfani ko ƙasa da ta karɓi wani kuɗi daga dukiyoyin Iran, ba za ta sami izinin wucewa ta mashigar ba.
-
Labarai Cikin Bidiyo | Yadda Sojojin Yemen Suka Kakkabo Jirgin Yaƙi "Bayraktar" Saudiyya
Kafofin yada labaran yaƙi sun watsa hotunan harbowa da tarkacen jirgin sa ido mai ɗauke da makamai na makiya Saudiyya, wanda sojojin Yemen suka harba a yau, a lokacin da yake gudanar da ayyukan liken asiri a sararin lardin Al-Jawf. Hotunan sun nuna tsarin sa ido da bin jirgin "Bayraktar Akinci" na ƙasar Turkiyya, da lokacin faɗuwarsa, baya ga hotunan tarkacen jirgin yana ci da wuta bayan faɗuwar sa a ƙasa. Kuma jirgin "Bayraktar" jirgi ne mara matuki na yaƙi mai muhimmanci daga nau'in masu tsayi da dogon zango, kuma an kera shi ne musamman don aiwatar da ayyukan kai hari na dabaru waɗanda a baya suka keɓanta ga jiragen yaƙi na gargajiya masu matuki kamar "F-16."
-
Yadda Sanya Takunkuman Makamai Na Kasashen Duniya Ya Gurgunta Da Illatawa Kan Ayyukan Yaƙin Isra’ila
Takunkuman kasashen duniya a cikin samar da makamai, kayan gyara da albarkatun ƙasa, sun zama barazana ta aiki ga sojojin gwamnatin yahudawa.
-
Ansarullah: Sojojin Yemen Sun Ƙara Ƙarfin Makamai Masu Linzami Na Musamman
Wani babban jami'in Ansarullah a Sana'a ya ce sojojin sun ƙara ƙarfin makamai masu linzami na musamman a kwanan nan ga makamansu waɗanda Yemen kaɗai ke da su.
-
Isra'ila Na Ci Gaba Da Kai Hare-Hare A Kudancin Lebanon, Tana Kona Da Rushe Gidaje A Bint Jbeil
Sojojin mamaya na "Isra'ila" sun kai hare-hare masu yawa a kudancin Lebanon a ranar Asabar, ciki har da kona da rushe gidaje a yankin Bint Jbeil, yayin da hukumomin siyasar Lebanon ke ci gaba da tattaunawa kai tsaye da "Isra'ila" ƙarƙashin jagorancin Amurka kan abin da ake kira "Tsararriyar Yarjejeniyar."
-
Sakon Jagora Ga Hizbullah
Jagora Sayyid Mujtaba Khamene'i: Kare Mujahidan Lebanon, Siyasar Dabaru Ce Ta Jamhuriyar Musulunci Ta Iran
Jagoran juyin juya halin Musulunci, a cikin wani sako, sun jaddada cewa: Jamhuriyar Musulunci ta Iran, a cikin manufar siyasar jagora shahidi, ta sanya kare waɗannan mujahidai masu ƙarfi da ake zalunta a matsayin muhimmiyar manufar dabaru.
-
Manazarcin Tsaro Kuma Masanin Harkokin Bayanai:
Nazari: CIA Tana Aiki Ne Ga Isra'ila, Ba Don Amurka Ba
John Kiriakou, manazarcin tsaro kuma masanin harkokin bayanan sirri, yana mai suka mai tsanani game da yanayin da CIA ke ciki a yanzu, ya yi iƙirarin cewa wannan hukuma ta shiga cikin tasirin ƙungiyoyin yahudawa sosai, kuma maimakon ta ci gaba da anfanar manufofin ƙasar Amurka, tana aiki ne don cimma manufofin Isra'ila.
-
UNOCHA: Karancin Kasafin Kuɗi Yana Barazana Ga Ayyukan Ciwarwa Ga Yara Da Mata Miliyan 5.7 A Afganistan
Ofishin Gudanar da Taimakon Bil'adama na Majalisar Ɗinkin Duniya ya yi gargadin cewa, karancin albarkatun kuɗi ya sanya samun damar yara da mata miliyan 5.7 a Afganistan ga ayyukan lafiya da abinci na yau da kullun cikin hadari mai tsanani.
-
MDD: Ta Jaddada Buƙatar Ɗaukar Matakin Gaggawa Don Tallafawa Mata Da 'Yan Mata Na Afganistan
Shugaban ofishin sashen mata na Majalisar Ɗinkin Duniya, a ziyararsa zuwa Afganistan, ya tattauna da jami'an Taliban da abokan huldar diflomasiyya game da ƙara tallafawa mata da 'yan mata, da kuma cire ƙuntatawa da aka sanya wa ma'aikatan mata na hukumomin jin kai.
-
Tonon Silili Yadda 'Yan Ƙasar Italiya Kusan 1,000 Su Kai Tarayya A Kisan Kiyashin Gaza
Hannun Kasar Italiya Dumu-Dumu A Kisan Kiyashin Da Isra’ila Ke Yiwa Falasdinawa
Bayanan hukumar ma'aikatar yaƙi na gwamnatin yahudawa da aka buga kwanan nan, sun nuna cewa 'yan ƙasar Italiya 928 sun shiga cikin kisan kiyashin da Isra’ila k yi a zirin Gaza daga Oktoba 2023 zuwa Maris 2025. Bayyana waɗannan takardun, waɗanda ke nuna haɗin gwiwar Rome da Tel Aviv fiye da dangantakar hukuma, ya haifar da cece-kuce mai yawa a cikin muhawarru na siyasa na Italiya, kuma Stefania Ascari, 'yar majalisar Italiya, ta zargi gwamnatin ƙasarta da gujewa daukar alhakin hakan.
-
Yahudawa Na Kai Harin Dabbancin Kan Fursunonin Matan Falasdinu A Kurkukun Al-Damun
Cibiyoyin kula da al'amuran fursunonin Falasdinu a yau (Lahadi) sun ba da rahoton faruwar wani aikin danniya mai tsanani a kan fursunonin mata na Falasdinu a kurkukun Al-Damun. Dangane da wannan rahoto, sojojin gwamnatin mamaya, ta hanyar kutsawa sashen mata a tsakiyar daren Juma'a, ta amfani da hayaki mai sa hawaye, duka da wulakanci, sun haifar da shaƙewar numfashi da kuma tsananta yanayin raunin jiki na wasu daga cikinsu. A halin yanzu, mata 94 na Falasdinu, ciki har da mata biyu masu juna biyu da marasa lafiya biyu masu ciwon daji, suna cikin wannan kurkuku.
-
Ayyukan Ta’addancin Yahudawa Na Kara Tsamari Bayan Kona Masallatai A Nablus Da Tulkarm
Ma'aikatar Harkokin Waje ta Hukumar Falasdinu, yayin da take yin Allah wadai da aikin yahudawa na kona masallatai biyu a ƙauyukan "Qasra" (Nablus) da "Kur" (Tulkarm), ta jaddada cewa waɗannan hare-hare suna faruwa ne tare da goyon bayan gwamnatin mamaya na Isra'ila kai tsaye, kuma saboda kariyar da ake bas u na rashin hukunta sun daga hukumar ne yasa suke wuce gon a da iri, kuma ta buƙaci al'ummar duniya ta ɗauki matakai masu tasiri da tilaswa don dakatar da waɗannan ta'addanci.
-
Rahoto Cikin Hotuna | Na Taron Tunawa Da Shahida Zahra Haddad Adel A Tehran
Rahoto Cikin Hotuna | Na Taron Tunawa Da Shahida Zahra Haddad Adel A Tehran
-
Menene Amurka Ta Yi Hasara a Makon Da Ya Gabata?
Girman Asarar Amurka A Fafatawar Mako Guda Da Iran
Rahotannin da kafofin watsa labarai na kasashen yamma suka buga a 'yan kwanakin nan sun nuna cewa fafatawar baya-bayan nan da Iran, ta haifar da hasarar rayuka da soji mai yawa ga Amurka a yankin, kuma ta yi tasiri ga lissafin rashin dabarar yakin Washington.
-
Labarai Cikin Hotuna | Na Taron Tunawa Da Shahidan Quds 2014 Karo Na 12 A Zaria
Sheikh Zakzaky {H}: Abin Alfahari Ne A Kashe Ka A Tafarkin Allah" / Muna Nan Daram A Tafarki Da Aka Kashe Waɗannan Shahidai.
-
Taron Tunawa Da Shahidan Quds 2014 Karo Na 12 A Zaria
Sheikh Zakzaky {H}: Abin Alfahari Ne A Kashe Ka A Tafarkin Allah" / Muna Nan Daram A Tafarki Da Aka Kashe Waɗannan Shahidai.
Jagora Shaikh Ibraheem Zakzaky (H) ya gabatar da jawabi a taron tunawa da waƙi'ar Ƙudus ta 25 ga watan Yulin 2014. Taron ya gudana ne a yau Asabar 25/7/2026 a muhallin Darur Rahma da ke Dambo, a Zariya.
-
Ansarallah: Yanzu Ba Lokaci Ne Na Maganar Sulhu Da Saudiyya Ba
Yamen: Ta Gudanar Da Babban Hari Na Biyu Mai Girma Na A Kan Aramco Bayan Shekaru 7
Kamfanin Aramco, babban kamfanin man fetur na duniya kuma ginshiƙin tattalin arzikin Saudiyya, a yau an kai masa hari a ayyuka guda biyu na sojojin Yemen a lokaci guda. An bayyana manufofin waɗannan hare-haren a matsayin matatar Jizan da cibiyoyin man fetur na Yanbu.
-
Sojojin Yemen Sun Sanar Hare-Hare Na Musamman Guda Biyu A Kan Cibiyoyin Aramco A Jizan Da Yanbu
Sojojin Yemen, tare da fitar da wata sanarwa, sun sanar da cewa, a martani ga hare-haren baya-bayan nan na Saudiyya a kan Al-Hudaydah da tsibirin Kamaran, da ci gaba da killacewar Yemen, sun gudanar da ayyuka biyu na soji a kan cibiyoyin Aramco a Jizan da Yanbu.