Shugaba Buharin ya bayyana haka ne a wata ganawa da yayi da 'yan Kungiyar Masarautar Daura da suka kai masa ziyara a gidansa da ke garin Daura, na jihar Katsina a jiya Litinin don yi masa ta'aziyyar rashin wasu danginsa biyu da yayi inda ya ce akwai kadarori masu yawa da gwamnati ta kwato da hannun barayin gwamnati wadanda mutanen da ake zargin na su ne suka musanta hakan, don haka gwamnatin za ta sayar da irin wadannan kadarori da sanya su cikin asusun gwamnati.
Shugaban na Nijeriya ya ce gwamnatin tana nan tana bin lamarin kayayyaki da kadarorin gwamnatin da aka sata daki-daki kamar yadda doka ta tanadar bisa tsari na demokradiyya, sai dai ya ce a wannan lokacin gwamnatin ba za ta bar lamarin ya tafi haka kawai ba, don kuwa a cewarsa: akwai wasu daga cikin masu satar dukiyar gwamnatin da aka kama, to amma wadanda suka ce wadannan kadarori ba na su ba ne, to gwamnati za ta sayar da su, a zuba kudin a asusun gwamnatin tarayya.
Shugaba Buharin yayi alkawarin gwamnati za ta yi iyakacin kokarinta wajen samar da takin zamani da sauran abubuwan da manoma suke bukata wajen ci gaba da bunkasa ayyukan gona, kamar yadda ya ce gwamnatin tasa za ta ci gaba da gina hanyoyi da layin dogo da kum samar da wutar lantarki wa al'ummar Nijeriyan kamar yadda ta yi alkawari.