22 Afirilu 2017 - 08:46
FIFA Da Kungiyar Man. UTD Sun Nuna Alhini Mutuwar Magoya Bayan Man United A Nijeriya

Hukumar kwallon kafa ta duniya (FIFA) da kuma kungiyar kwallon kafa ta Manchester United ta kasar Ingila sun bayyana bakin ciki da kuma aihininsu dangane da mutuwar wasu magoya bayan kungiyar su kimanin 30 a birnin Calabar, na Jihar Cross River da ke kudancin Nijeriya sakamakon fadowar wani layin wutar lantarki a kansu.

A cikin wasu sakonni mabambanta da suka fitar, hukumar ta FIFA da kuma  kungiyar Manchester United din sun bayyana alhini da kuma ta'aziyyarsu ga 'yan uwa da iyalan wadanda lamarin ya rutsa da su a ranar Alhamis din da ta gabata.

Shi ma a nasa bangaren, shugaban Nijeriya Muhammadu Buhari, ta bakin kakakinsa Garba Shehu, ya ce ya kadu kwarai da jin labarin abin da ya faru wanda ya janyo asarar rayuka da dama. Don haka shugaban ya ce yana isar da sakon ta'aziyyarsa ga iyalan wadanda abin ya shafa, da kuma gwamnati da jama'ar jihar Cross River, haka zalika da masoya kwallon kafa a duk fadin Nijeria.

Wannan lamari dai ya faru ne ranar Alhamis din da ta gabata da daddare a lokacin da jama'a suka taru makil a wani gidan kallon talabijin a birnin na Calabar don kallon wasan kwallon kafa na Europa tsakanin kungiyar Manchester United da Anderletch ta kasar Belgium inda wani babban layin wutar lantarkin ya katse da kuma fadowa kan jama'a inda aka ce alal akalla mutane 30 sun mutu.288