Shugabannin sun bukaci haka ne a taron ECOWAS na 50 da suka gudanar a birnin Abuja na Najeriya, in da suka mafi mayar da hankali kan rikicin siyasar Gambia.
Tuni dai Jammeh ya shigar da kara a kotun koli don kalubalantar sakamakon wanda ya amice da shi a farko kafin ya bijire daga bisani.
A farkon makwannan ne dakarun Jammeh suka kwace hukumar zaben kasar, abin da ya janyo masa suka daga kasashen duniya.288