10 Afirilu 2015 - 11:38
Da'ish ta yi garkuwa da mutane 50 a Syria

kungiyar Da'ish sun yi garkuwa da mutane akalla 50 yawancinsu Mata a yankin Hama cikin kasar Syria kamar yadda kungiyar da ke sa ido a rikicin kasar ta ruwaito. Kungiyar ta ce mayakan sun yi garkuwa da mutanen ne a kauyen Mabujeh da ke tsakiyar Syria tun a ranar 31 a watan Maris, amma an yi shiru da batun sace su saboda tattaunawar kokarin kubutar da su.

Babban Jami’in kungiyar da ke sa ido a rikicin Syria Rami Abdel Rahman ya ce babu wani haske a tattaunawar neman kubutar da mutanen.

Kungiyar tace mutanen da aka kama ‘yan Ismailis ne da keda alaka da Shi’a.

Kungiyar Da'ish dai ta dade tana kai wa kabilun Syria harii da suka hada da ‘Yan Jazidi da Assyrian kiristocin Syria kuma Alawites kabilar shugaba Bashar al Assad.ABNA.