16 Maris 2015 - 08:03
shugaban Ansarullah ya gana da manema labarai

Abdulmailik Husi; wasu kasashen suna kashe makudan kudi domin kawo cikashi ga tattaunawar kasa dake gudana a Yaman

Kamfanin dillancin labarai na Ahlulbaiti{A.S}-abna-shugaban Ansarullahi na Yaman a wata hira da yayi da manema labarai a garin Sa'ada yace, hudar kasar Yaman da sauran kasashe ya ginu ne a bisa tsari na girmama juna da rashin tsoma baki ga al'amuran da suka shafi cikin gida.

Abdulmailik Husi ya kara da cewa, muna farin ciki a bisa huda da kowace kasa ta larabawa ko  ta musulmi tare da girmama juna da rashin shiga al'amuran da suka shafi siyasar kasar.

A wani bangaran ya yi tsokaci a bisa taimakon da wasu kasashe ke yima tsohon shugaban kasar wato Mansur Hadi domin kawo cikas ga tattaunawar kasa dake gudana a yanzu.ABNA