2 Faburairu 2015 - 10:47
Hamas na neman taimakon Iran

Wani babban jami'in kwakwarmayar musulunci ta Falastin{Hamas} ya bukaci taimakon Jamhuriyar musulunci ta Iran domin kawo karshen mamayar da HK.Isra'ila tayima yankin.

Kamfanin dillancin labarai na IRINN-Mahmud zahar wani babban jami'I na Hamas yace; kungiyar Hamas a shirye take domin yin aiki da Iran wajan kawo karshen mamayar da yahudawan sahayoniya suka yimasu.

Zahar a cikin hirar da yayi da gidan talabijin na Almanar Lebanon ya bukaci da Iran ta taimaka domin su fita halin da suka shiga na kaka nikayi.

Wata jarida ta sahayoniya tace, wannan kiran da jami'in Hamas ya ga Iran na nuni da jawarcin da kungiyar kema Iran domin kulla sabuwar zumunta.ABNA