11 Yuli 2026 - 19:01
Source: Hauza
Sayyid Ali Khumaini: Duk Wanda Yayi Tattaunawa Da Amurka Domin Yin Sulhu Maha'inci Ne + Bidiyo

Hujjatul Islam Sayyid Ali Khumaini ya jaddada cewa tsayuwar al'ummar Iran da goyon bayan da suka bai wa dakarun tsaro ne ya ba Jamhuriyar Musulunci damar shawo kan mawuyacin hali, yana mai cewa babban abin da Shahidin Jagora ya bari shi ne kare da kuma ƙarfafa akidar Juyin Juya Halin Musulunci.

Kamfanin Dillancin Labaran ƙasa da ƙasa na Ahlul-Baiti (AS) – ABNA – bisa nakaltowa daga Kamfanin Dillancin Labaran Hauza ya bayar da rahoton cewa: Jikan Imam Khumaini (Q), Hujjatul Islam Sayyid Ali Khumaini ya bayyana hakan ne da yammacin Juma'a yayin taron tunawa da Shahidin Jagora, Ayatullah Sayyid Ali Khamene'i (R.A.), wanda aka gudanar a Hubbaren Sayyida Fatima Ma'asuma (A.S.) da ke birnin Qum.

Ya ce har yanzu rashin Shahidin Jagora babban rashi ne ga al'ummar Iran, amma a cikin mawuyacin lokacin da ƙasar ta shiga, jama'a sun tsaya tsayin daka tare da dakarun tsaro, lamarin da ya rusa dukkan shirye-shiryen maƙiya.

Hujjatul Islam Sayyid Ali Khumaini ya yaba da rawar da jama'a suka taka, yana mai cewa Jamhuriyar Musulunci ta samu kariya ne saboda sadaukarwa da jajircewar al'umma. Ya kuma yi gargadin cewa bai dace ba bayan an shawo kan rikici a rika kiran mutanen da suka kare ƙasa da sunaye irin su "masu tsattsauran ra'ayi" ko "masu wuce gona da iri."

Ya bayyana kashe Shahidin Jagora a matsayin babban cin mutunci ga Iran da al'ummarta, yana mai cewa duk wani jami'in gwamnati da ba ya tunanin ɗaukar fansar jininsa, ya kamata ya sake nazarin lamirinsa da nauyin da ke kansa.

Haka kuma ya ce wajibi ne a rika yin Allah wadai da masu hannu a wannan laifi da kuma masu goyon bayansu a dukkan tarukan tunawa da Shahidin Jagora, yana mai jaddada cewa sunansa da tafarkinsa za su ci gaba da rayuwa a zukatan al'ummar Iran.

Jikan Imam Khumaini (R.A.) ya bayyana cewa babbar nasarar Shahidin Jagora ita ce kiyaye da ƙarfafa akidar Juyin Juya Halin Musulunci, wadda ta samo asali daga zurfin imanin al'umma kuma ta ci gaba da ƙarfafuwa a ƙarƙashin jagorancinsa.

Da yake magana kan abubuwan da suka faru a baya-bayan nan, ya ce Jamhuriyar Musulunci ta nuna tsayin daka a gaban matsin lambar Amurka da Isra'ila, yana mai ƙara da cewa bai kamata a ɗauki tattaunawa daidai da sulhu ba.

A ƙarshen jawabinsa, Hujjatul Islam Sayyid Ali Khumaini ya gode wa al'ummar Iran, mawaƙan yabon Ahlul Baiti (A.S.) da kuma haɗin kan al'ummomin Iran da Iraki wajen girmama Shahidin Jagora, tare da jaddada muhimmancin ci gaba da kare manufofin Juyin Juya Halin Musulunci.

.......................

Tags

Your Comment

You are replying to: .
captcha