18 Nuwamba 2025 - 08:22
Source: ABNA24
Riyadh: Shugaban Iran Ya Aikewa Da Yarima Saudiyya Saƙon Wasika

Hukumar Yaɗa Labarai ta Saudiyya ta sanar da cewa Yarima Mai Jiran Gado Na ƙasar ya karɓi saƙon rubutu daga Shugaban Iran.

Kamfanin Dillancin Labaran ƙasa da ƙasa na na Ahlul Baiti (AS) – ABNA– ya habarto cewa: Yarima Mai Jiran Gado Na Saudiyya Mohammed bin Salman bin Abdulaziz Al Saud ya karɓi saƙon rubutun wasika daga Shugaban Iran Masoud Pezzekian a ranar Litinin.

A cewar Kamfanin Dillancin Labarai na Saudiyya (SPA), an isar da saƙon ga ɓangaren Saudiyya a lokacin wani taro tsakanin Alireza Rashidian, shugaban ƙungiyar Hajji da ziyara ta Iran, da Abdulaziz bin Saud bin Nayef bin Abdulaziz, Ministan Harkokin Cikin Gida na Saudiyya.

A lokacin taron, ɓangarorin biyu sun tattauna batutuwa da dama da suka shafi juna. Alireza Enayati, jakadan Jamhuriyar Musulunci ta Iran a Saudiyya, shi ma ya halarci taron.

Your Comment

You are replying to: .
captcha