ABNA24 : Williams ta kara da cewa sakamakon taron da ya gabata yana da kyau sosai, don dukkanin mutane 75 da MDD ta zaba don halattan taron sun amince da zabubbuka wadanda za’a gudanar a shekara mai zuwa.
Sannan ta kara da cewa idan sun dawo a makon mai zuwa zasu tattauna kan tsarin da za’a gudanar da zaben na shekara mai zuwa.
MDD ce ta zami mutane 75 daga bangarori daban-daban na kasar don tabbatar da cewa duk mutanen kasr sun sami wakilci a taron.
An gudanar da taron na Tunisia ne bayan da aka dakatar da budewa juna wuta a cikin kasar ta Libya a cikin watan Octoban da ya gabata.(19)
342/