15 Janairu 2022 - 19:32
Nigeriya: Hukumar Zabe Ta Sanya Ranar 26 Ga Watan Fabrairu A Matsayin Ranar Zaben Cike Gurbi

Hukumar Zabe mai zaman kanta a tarayyar Najerita ta bada sanarwan cewa zata gudanar da zabubbukan cike-gurbi na wasu kujerun ‘yan majalisar dattawa da na wasu majalisun jihohi a ranar 26 ga watan fabrairu mai zuwa.

Kamfanin dillancin labarai na Ahlul-Baiti {a.s} - ABNA - ya bayyana cewa hukumar ta tsaida wannan ranar ne a wani taron da aka gudanar a jiya Jumma’a ta kuma kara da cewa jihohi 4 ne abin ya shafi kuma sun hada da Ondo, Plato, Imo da kuma Cross rivers.

342/