Kamfanin dillancin labarai na Ahlul-Baiti {A.S} - ABNA :Wannan dai shi ne sakamakon farko na zaben ‘yan majalisar dokokin da aka gudanar a kasar ta Morocco a ranar jiya Laraba.
Jam’iyar RNI wacce wani hamshakin attajiri kuma tsohon ministan noma na kasar, Aziz Akhannouch yake jagoranta ta sami kujeru 97 daga cikin kujeru 395 na majalisar dokokin kasar, biye da ita akwai Jam’iyyar PAM mai kujeru 82 daga nan sai jam’iyyar Istiqlal mai kujeru 78. Jam’iyyar PJD dai ta sami kujeru 8 ne kacal bayan an irga kashi 96% na kuri’un da aka kada.
342/