Kamfanin dillancin labarai na Ahlul-Baiti {A.S} - ABNA : Tashar Talabijin ta Presstv a nan Tehran ta bayyana cewa, Janar Qa’anin ya gana da kwamitin tsaro na majalisar dokokin kasar Iran a jiya Talata a asirce, inda ya bayyanawa kwamitin yadda ya ke fahintar rikicin kasar Afganistan a halin yanzu., musamman bayan karbar Taliban iko da kasar.
Kakakin kwamitin tsaro na majalisar dokokin kasar Iran, Seyyed Nizamuddin Mousawi ya fadawa ‘yan jarida bayan taron na jiya, kan cewa matsayin Iran dangane da abinda ya ke faruwa a kasar Afganistan a fili yake, kuma shi ne matsayin Imam Sayyid Aliyul Khamina’i Jagoran juyin juya halin musulunci a kasar, kan cewa Iran ba za ta nada hannayenta ta na kallon al-amura suna tabarbarewa a makobtanta na gabas ba.
Don tsaro da zaman lafiya a kasar Afganistan, shi ne tsaro da zaman lafiya a kasar Iran.
342/