29 Agusta 2021 - 10:26
ECOWAS Ta Yaba Da Dage Takunkumi Kan Tsaffin Shugabanin Rikon Mali

Kwamitin kula da mika mulki a kasar Mali, ya yi maraba da matakin gwamnatin riko na kasar, na dage takunkuman da ta kakabawa tsohon shugaban rikon kwarya, Bah N’Daw da Firaministansa Moctar Ouane.

Kamfanin dillancin labarai na Ahlul-Baiti{A.S} - ABNA : Wata sanarwa da kwamitin ya fitar, ta kuma yi maraba da matakan da gwamnatin ta dauka na tabbatar da sun amfana daga hakkokin da suke da shi a matsayinsu na tsohon shugaban kasa da tsohon Firaminista.

Bayan maraba da matakin kwamitin yankin mai kula da mika mulki a Mali, ya kuma jaddada goyan bayansa kan mulkin rikon kwarya na kasar ta mali.

Nan gaba a mako mai zuwa ne ake sa ran babban mai shiga tsakani, na kungiyar ECOWAS, kan rikicin Mali, tsohon shugaban Najeriya, Goodluck Jonathan, zai kai wata ziyara a kasar Malin.

342/