14 Maris 2021 - 14:05
​Libya:Majalisar Shugabancin Kasar Tana Kokarin Fitar Da Kasar Daga Matsaloli

Sabon shugaban majalisar mulki ta kasar Libya ya bayyana cewa majalisarsa za ta yi duk abinda zata iya don ganin ta fudda kasar daga matsalolin da ta dade tana fama da su.

ABNA24 : Kamfanin dillancin labaran ISNA na kasar Iran ya nakalto shugaban majalisar Muhammad Al-manfi ya na fadar haka a wani jawabin da ya gabatar a tashar talabijin ta kasar.

Al-manfi ya kara da cewa majalisarsa za ta yi kokarin ganin an dawo da zaman lafiya a kasar Libya sannan mutanen kasar a cikin ‘yenci zasu kafa tsarin democradia wacce za ta lamuncewa ko wani dan kasar hakkinsa.

A wani taro, wanda majalisar dokokin kasar ta Libya ta gudanar a birnin Sirt a ranar Laraban da ta gabata ce wakilan majalisar 132 suka zabi Al-manfi sabon shugaban riko wanda zai hada kan mutanen kasar ya kuma azata kan turbar democradiyya.

342/