ABNA24 : Gidan radiyon Faransa ya bayar da rahoton cewa, a lokacin da ake nasarar hukumar ta WFP a birnin Oslo na kasar Norway, shugaban kwamitin bada lambar yabon ta Nobel Berit Riess-Andersen, ya ce annobar corona ta kara tsananta halin yunwa da mutane suke ciki a wasu sassa na duniya.
Riess-Andersen ya kara da cewa, suna fatan ganin mutanen duniya sun karkata idanunsu domin ganin halin yunwa da wasu ke ciki a wasu kasashen duniya.
Hukumar samar da Abinci ta Majalisar Dinkin Duniya ita ce kan gaba wajen ayyukan jinkai a duniya, inda take taka muhimmiyar rawa wajen samar da abinci ga mutane sama da miliyan 690, dake fama da yunwa.
Matsalolin yake-yake da tashe-tashen hankula da fari na daga cikin abubuwan da suke jefa al’ummomi cikin matsanancin talauci da rashin abinci, kamar yadda kuma a wannan shekara bullar cutar corona ta taimaka wajen mayar da hannun agogo baya a harkokin noma da kasuwanci a duniya, wanda ya yi babban tasiri wajen kara tsanantar wannan matsala.
342/