21 Satumba 2020 - 12:18
Najeriya : PDP, Ta Lashe Zaben Jihar Edo Da Gagarimin Rinjaye

Hukumar zabe mai zaman kanta a Najeriya (INEC), ta sake tabbatar da Godwin Obaseki na Jam'iyyar adawa ta PDP a matsayin wanda ya lashe zaben gwamnan jihar Edo.

ABNA24 : Gwamna Obaseki ya dai doke abokin hamayarsa na Jam'iyyar APC, Fasto Osagie Ize-Iyamu, kuma wannan shi ne karo na biyu da Obaseki ke doke Ize-Iyamu, amma lokacin Obaseki na APC, shi kuwa Ize-Iyamu yana a PDP.

Hukumar ta INEC ta bayyana cewa Mista Obaseki ya samu kuri'u dubu 307 da 955 inda kuma Mista Osagie Ize-Iyamu ya samu kuri'u dubu 223 da 619 a ciikin adadin kuri'un da aka jefa 550,242

Ana dai kallon zaben na jihar Edo, tamkar wani zakaran gwajin dafi ne tsakanin APC da PDP.

342/