15 Satumba 2020 - 12:15
Majalisar Gwamnonin IAEA Ta Fara Taronta Na Watan Satumba

A yau Litinin ce majalisar gwamnoni ta hukuma mai kula da al-amuran makamshin nukliya a duniya IAEA ta fara taronta a birnin Vienna na kasar Austria.

ABNA24 : Kamfanin dillancin labaran Farsnews na kasar Iran ya nakalto jakadan kasar Rasha a hukumar Mikhail Awliyonuv yana fadar haka a shafinsa na twitter . Ya kuma kara da cewa an gudanar da taron ne a babban dakin taro na hukumar saboda hana yaduwar korona a tsakanin mahallata taron.

Agendar taron gwamnonin dai sun hada da yarjejeniyar JCPOA ta kasar Iran da kuma batun harkokin tsaro a yankin kudancin Asia.

Har’ila yau za ta tattauna dangane da matakan da kasar Iran take dauka na jingine wasu alkawulan da ta dauka a yarjejeniyar JCPOA kamar yadda maddoji na 26 da kuma 36.

342/