22 Yuli 2020 - 11:21
​Sudan : An Dage Shari’ar Da Ake Wa Al-Bashir Har Zuwa Ranar 11 Ga Watan Agusta

A Sudan, an dage shari’ar da ake wa tsohon shugaban kasar Umar Al’bashir har zuwa ranar 11 ga watan Agusta mai zuwa.

ABNA24: An dai dage shari’ar ce awa guda bayan soma ta saboda rashin isashen wuri a cikin farfajiyar kotun.

A jiya ne hambararen shugaban kasar ya sake bayyana a gaban kotun Khartoum, a wannan karo kuwa bisa tuhumarsa da kwace mulki ta hanyar amfani da tsinin bindiga shekaru 31 da suka gabata.

A ranar 30 ga watan Yunin shekara 1989 ne, Al’Bashir ya kifar da gwamnatin Sadek el-Madhi.

Baya ga Al’bashir din da akwai wasu tsafin jami’an gwamnati da manyan sojoji 27 da su ma ake ma irin wannan tuhuma.

342/