Taskar watsa labarai ta Ahlul-Baiti-ABNA24-ta rawaito cewa; Shugaban kasar Iran Dr Hassan Rouhani ya rattaba hannu kan dokar da majalisar dokokin kasar ta yi wa gyara, wacce kuma ta fadada dokar wacce aka samar da ita a cikin watan Afrilun shekarar da ta gabata, don ta game dukkan sojojin Amurka a duniya, a matsayin hukumar yan ta’adda.
Kafin haka dai gwamnatin Amurka da sanya IRGC a matsayin kungiyar yan ta’adda a shekarar da ta gabata, sai Iran kuma ta kafa dokar maida sojojin Amurka a yankin gabas ta tsakiya wato United States Central Command (CENTCOM) a matsayin yan ta’adda sannan bayan kisan Janar Sulaimani majalisar dokokin kasar ta fadada ta zuwa kan dukkan sojojin Amurka.
14 Janairu 2020 - 09:52
Lambar labari: 1002258
Shugaban Kasar Iran Hassan Rauhani ya4 rattaba hannu kan wata doka da ta maida Pentagon hukumar yan ta'adda