Kamfanin dillancin labaran AFP na kasar Faransa ya nakalto Edward Kallon jami'in hukumar bada agaji ta majalisar dinkin duniya a Najeriya yana fadar haka a jiya Laraba.
Edward ya kara da cewa a cikin makon da ya wuce kadai mutane kimani dubu 30 ne suka kauracewa gidajensu a garin Baga zuwa birnin Maiduguri inda ake da sansanonin yan gudun hijira, sanadiyyar tsananin fadan da ake fafatawa tsakanin sojojin kasar da kuma mayakan kungiyar Boko Haran a yankin.
Gwamnatin Najeriya dai ta amince akwai matsalolin yan ta'adda a yankin gabacin jihar Borno amma tace sojojin kasar sun fi karfin mayakan na Boko haram a mafi yawan yankunan jihar ta Borno idan an kwatantan da yadda aka sami yankin a lokacinda ta haw kan kujerar ikon kasar.