Kwamitin ya bayyana haka ne a wani rahoto da ya mika wa shugabannin kungiyar a yayin gudanar da taronsu karo na 54 a birnin Abuja karkashin jagorancin shugaban Najeriya, Muhammadu Buhari.
A yayin zantawa da manema labarai, Ministan Harkokin Wajen Nijar kuma daya daga cikin mambobin kwamitin Kalla Hankurau, ya ce, lallai akwai bukatar gaggauta samar da kudin na bai daya don bunkasa tattalin arzikin yankin.