Kamfanin dillancin labarun Faransa ya ce; "Yan tawayen sun kai hari ne a wata makaranta da take gartin Bafut a yankin arewa maso yammacin kasar.
Rahotanninn farko sun ambaci cewa sojoji 8 ne su ka bace, sai dai an saki uku daga cikinsu daga baya.
Yankunan da suke magana da harshen Ingilishi a kasar ta Kamaru da suka hada gundumomin arewa maso yamma da kuma kudu maso yamma, sun fara daukar makamai ne a shekarar da ta gabata ta 2017.
Mazauna yankunan suna zargin gwamnatin kasar da nuna musu wariya bisa dalilai na harshen da suke magana da shi a yankin.
Adadin masu magana da harshen na Ingilishi a yankunan biyu sun kai kaso 20 % na jumillar mutanen kasar miliyan 20.