Sanarwar ta Majalisar dinkin duniya a Juma’ar da ta gabata, ta bayyana janye jami’anta baki daya guda 40 da ke ayyukan agaji a sansanin na Rann mai dauke da ‘yan gudun hijira akalla dubu 55,000.
Zalika an dakatar da kai kayayyakin agaji zuwa sansanin ‘yan gudun hijirar.
A daren ranar Juma’a itama kungiyar Likitoci ta kasa da kasa Medecins sans Frontieres ta sanar janye ayyukanta a sansanin na Rann, sakamakon harin na mayakan Boko Haram.