21 Maris 2026 - 21:58
Source: ABNA24
Iran Ta Kai Munanan Hare-Hare Akan Wurare A Cibiyar Nukiliyar Dimona Da Hamadar Naqb + Bidiyo

A cikin sabbin hare-haren da sojojin Jamhuriyar Musulunci ta Iran suka kai, yankunan Dimona da hamadar Naqb sun kai munanan hare-hare da makamai masu linzami inda saboda tsananin asarar da suka haifar an ga saukar jirgin yakin Isra’ila domin kwashe wanda harin ya shafa.

Kamfanin Dillancin Labaran ƙasa da ƙasa na Ahlul-Baiti (ABNA) ya ruwaito cewa: A hare-haren na baya-bayan nan na sojojin Jamhuriyar Musulunci ta Iran, yankunan da ke Dimona da hamadar Naqb sun kai harin da makamai masu linzami.

Kamar yadda majiyoyin labarai suka tabbatar da cewa hare-haren sun aukawa wurare 12 a Dimona ya zuwa yanzu. A lokaci guda tare da aukuwar munanan hare-haren da Iran ta kai kan yankunan da aka mamaye, an yi gaggawar bugawa tare da yada hotuna da bidiyoyin wannan harin makamai mai linzami a shafukan sada zumunta.

An bayar da rahoton cewa, Iran ta kai hari kan wani gini a cibiyar nukiliyar Dimona ta Isra'ila, lamarin da ya yi sanadin jikkata da dama. Gwamnatin sahyoniyawan ba taki bari a bayar da wani bayani kan adadin wadanda su rasa rayukansu. An kai hare-haren ne a matsayin martani ga harin da Amurka da Isra’ila suka kai cibiyar nukiliyar Natanz a yau.

Alamomi

Ra'ayinka

You are replying to: .
captcha