Kamfanin Dillancin Labarai na Ahlul-Bayt (a.s) - ABNA – ya bayar da rahoton cewa: Sojojin Yemen a cikin sanarwarsu sun sanar da cewa, aikin farko, ya kai hari a kan muhimman cibiyoyin Aramco a Jizan da makamai masu linzami na ballastic da jirage mara matuki da dama, kuma a aiki na biyu, an kai hari a kan cibiyoyin Aramco a Yanbu da makamai masu linzami na ballastic, cruise da jirage mara matuki.
A cikin wannan sanarwa an yi iƙirarin cewa, dukkan ayyukan biyu an yi su da daidaito da nagarta, kuma sun kai hari a kan manufofin da aka kayyade.
A cikin wannan sanarwa, hare-haren sama na baya-bayan nan na Saudiyya a kan birnin da tashar jiragen ruwa na Al-Hudaydah da tsibirin Kamaran, an bayyana su a matsayin dalilin aiwatar da waɗannan ayyukan.
Sojojin Yemen sun yi iƙirarin cewa, waɗannan hare-hare sun haifar da asara ta jiki da ta tunani, kuma tsarin tsaron Yemen sun yi artabu da jiragen masu kai hari dake kokarin hana ci gaba da kaihare-haren.
Sojojin Yemen, tare da yin nuni ga ci gaba da killacewar ƙasarsu, sun sanar da cewa, tsananta matakan Saudiyya, zai ƙara azamar Sana'a na fuskantar ta.
A cikin wannan sanarwa an jaddada cewa, sojojin Yemen za su ci gaba da kare ƙasarsu da al'ummarsu a gaban abin da ake kira "ta'addanci," za su tsaya daga matsayin ƙarfi.
……………….
Ra'ayinka