Kamfanin Dillancin Labaran ƙasa da ƙasa na na Ahlul Baiti (AS) – ABNA– ya habarto cewa: Falasdinawa na ci gaba da gudun hijirar daga Gaza zuwa kudanci da kuma wuraren da suke da tsaro a karkashin munanan hare-haren da Isra'ila ke kai wa. Rahotanni sun nuna cewa da yawa daga cikin wadannan ‘yan gudun hijira na fuskantar matsalar karancin ruwa, abinci, da matsuguni a kan doguwar tafiya mai hatsarin gaske, kuma kasashen duniya sun yi gargadin illar da wannan hijirar dolen zata haifar.






Your Comment