2 Nuwamba 2020 - 14:37
Iran: An Fara Daukar Matakai Masu Tsauri Don Dakile Cutar Korona Daga Yau Litinin

A yau ne gwamnatin kasar Iran za ta fara daukar Karin matakan masu tsauri don dakile yaduwar cutar korona a kasar, wacce ta ke kashe daruruwan mutane a ko wace rana a cikin makonnin da su ka gabata.

ABNA24 : Sabon tsarin wanda zai shafi larduna 25 cikin jimillar larduna 31, zai hana dukkan ababen hawa fita daga Lardunansu na asali, sannan zai hana masu zuwa daga wasu larduna shiga wani lardi na daban. Wato zirga-zirgan ababen hawan, zai takaita ne a cikin larduna kadai.

Har’ila yau takaida zirga-zirgan zai fara ne daga yau Litinin har zuwa ranar jumma’a ami zuwa 6 ga watan Nuwamba.

Tashar talabijin ta Presstv ta nakalo kakakin ma’aikatar kiwon lafiya ta kasa Simo Saadat Lara ta na cewa a jiya Lahadi kadai mutane 434 ne cutar ta kashe a duk fadin kasar, sannan wasu 7,719 suka kamu da ita.

342/