31 Mayu 2016 - 10:34
‘Yan sanda sun yi arangama da ‘Yan Biafra

Akalla mutane bakwai aka tabbatar da mutuwarsu a arangamar da aka yi tsakanin jami’an tsaro da masu fafutukar kafa kasar Biafra a Asaba da ke Jihar Delta.

Kakakin ‘Yan Sandan Jihar Charlse Muka ya ce jami’an soja sun harbe biyar daga cikin masu fafutukar bayan sun kai hari kan ‘Yan Sanda suka kuma kashe biyu daga cikin su, tare da raunana wasu.

Rahotanni sun ce masu fafutukar sun kuma kai hari kan matafiya a hanyar Asaba zuwa Onitsha.

Amma ‘Yan sanda sun cafke wasu da dama daga cikinsu a Jihohin Enugu da Imo da ke yankin kudu masu gabashi.288