15 Faburairu 2016 - 06:33
Syria ta yi Allawadai da matakin Turkiyya

Syria ta ce hare-haren da Turkiyya ke kaiwa kan wasu wuraren da mayakan Kurdawa suka kame a cikin kasar Syriar keta hakkin Syriar ne, tana bukatar Majalisar dinkin duniya da ta dauki mataki.

Haka kuma Syriar ta zargi Turkiyya da kyale wasu 'yan bindiga dari suka shiga kasar Syriar.

Sai dai Firayim Ministan Turkiyya Ahmet Davutoglu ya ce kasarsa ta ta ci gaba da luguden boma-bomai a kan wuraren da Kurdawa suka kame a kan iyakar Turkiyya da Syria.

Turkiyyar ta bayana cewa kungiyar Kurdawa ta PYD na da alaka da mayakan sari-ka-noke na kungiyar PKK wadanda suka kwashe shekaru suna fada da gwamnatin Turkiyya.

Sai dai Amurka ta yi watsi da matsayin Turkiyya, tana kallon kungiyar PYD a matsayin kawar da za ta yi tasiri wajen yakar kungiyar IS a Syria.288