Ana zargin 'yan Boko Haram da kaddamar da wadannan hare-haren.
Bayanai sun ce an tayar da bam guda a kasuwar garin da kuma daya a wurin binciken ababen hawa.
"Akalla mutane 10 sun rasu, a yayin da fiye da 30 suka samu raunuka," in ji Ayuba Chibok.
A garin na Chibok ne a 2014 aka sace 'yan mata dalibai su sama da dari biyu, wadanda har yanzu ba aji duriyar galibinsu ba.288