30 Nuwamba 2024 - 06:19
Abubuwan Da Ke Faruwa A Siriya; Rasha Na Ci Gaba Da Kai Hare-Hare Kan Wuraren 'Yan Ta'addar Halab

A ranar 28 ga watan Nuwamba, sojojin Turkiyya sun bukaci kwamandojin kungiyoyinsu masu biyayya da su aike da sojoji zuwa yankunan da ke kusa da Manbij da kuma layukan tuntuɓar hukumar soji ta Manbij, mai alaƙa da "QSD".

A wata hira da kamfanin dillancin labarai na Reuters, majiyoyin sojan Syria 2 sun sanar da cewa, Damascus na jiran aikewa da kayan aikin sojan kasar Rasha a sansanin sojin sama na Hmeimim dake kasar Syria cikin sa'o'i 72 masu zuwa.

Wakilin tashar Al-Mayadeen ya kuma bayar da rahoton cewa, 'yan ta'adda sun kwace fiye da kashi 40% na yankunan yammacin birnin Halab da ke arewacin kasar Siriya.

Wata majiyar soji ta kuma sanar da rufe filin tashi da saukar jiragen sama na Halab tare da soke dukkan zirga-zirga a wannan filin jirgin.

Wakilin Aljazeera ya bayar da rahoton cewa, an ci gaba da gwabza fada tsakanin 'yan ta'adda da sojojin Syria a kewayen Halab da kuma makarantar horas da sojoji ta birnin a cikin 'yan sa'o'i da suka gabata.

sojojin kasar Rasha su na ci gaba da kai hare-hare ta sama da kan yankuna daban-daban na Halab ciki har da Ma'er da ke yammacin Halab.

An kashe mutane 4 a harin da mayakan Rasha suka kai kan hedkwatar dakarun da ke da alaka da Turkiyya a arewa maso yammacin Siriya

A safiyar yau Asabar ne wani jirgin yakin kasar Rasha ya kai hari kan hedikwatar sojojin kungiyar "Hadin gwiwar sojojin" da ke da alaka da rundunar sojin kasar Syria da ke samun goyon bayan Turkiyya a yankin Mar'a da ke arewacin Halab.

Wannan harin ta sama da aka kai da makamai masu linzami guda uku, ya kai ga lalata hedikwatar da motocin soji da dama.

A ranar 28 ga watan Nuwamba, sojojin Turkiyya sun bukaci kwamandojin kungiyoyinsu masu biyayya da su aike da sojoji zuwa yankunan da ke kusa da Manbij da kuma layukan tuntuɓar hukumar soji ta Manbij, mai alaƙa da "QSD".

A lokaci guda tare da isar da dakarun da ke da alaka da Turkiyya, sojojin na Rasha sun kuma bar sansanonin soji a Tal Rifat da filin jirgin saman soja na Mengh.

Wadannan hare-hare sun ƙara haifar da damuwa game da yiwuwar sake kai wani sabon hari a wannan yanki.